ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Barau Ya Gargaɗi Gwamna Abba Kan Siyasantar Da Batun Tsaro A Kano

by Abubakar Sulaiman
6 months ago
Barau

LABARAI MASU NASABA

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

‘Yan Majalisar Wakilai 6 Daga Oyo Sun Fice Daga PDP Zuwa APM

A wani sabon martani da ya fito daga ofishinsa, Mataimakin Shugaban Majalisar Dattawa, Sanata Barau I. Jibrin, ya yi kira ga Gwamnan Kano Abba Kabir Yusuf da ya daina siyasantar da batun tsaro, yana mai cewa abin da ake buƙata shi ne aikin gwamnati mai ma’ana don magance matsalolin da suke addabar jihar. Wannan na zuwa ne bayan gwamnatin jihar ta zargi Sanata Barau da yin magana da ka iya kawo cikas ga ƙoƙarin tsaro, zargi da ya ce ba shi da tushe balle makama.

Sanata Barau, ta bakin mai magana da yawunsa Ismail Mudashir, ya ƙalubalanci gwamnati da ta fito fili ta nuna bidiyon da ake cewa ya yi magana da ke tayar da tarzoma. Ya jaddada cewa a dukkan lokuta yana aiki tare da hukumomi da sauran masu ruwa da tsaki wajen magance barazanar ƴan fashi da hare-haren da ake fuskanta a wasu sassan jihar Kano da ƙasar baki ɗaya. Ya bayyana cewa gwamnatin jihar ta karkatar da hankalinta daga gudanar da mulki yadda ya kamata zuwa yaɗa kalaman da ba zasuyi  amfani ga al’umma.

  • Barau Zai Yi Ƙarar Kwamitin Yaƙin Neman Zaɓen Gawuna/Garo Kan Zargin Karɓar Cin Hancin Dala Miliyan 10
  • ‘Yansanda Sun Ƙaryata Rahoton Kashe Ɗan Wasan Barau FC A Katsina

Sanata Barau ya ce rashin daidaito a gwamnati ya sanya Kano ta rasa matsayinta na zama sahun gaba wajen ci gaba a Nijeriya, inda ya buƙaci Gwamna Abba ya tashi tsaye wajen mayar da jihar kan tafarkin ci gaba. Ya kuma yi nuni da gudunmawar da ya bayar a fannin tsaro, ciki har da samar da motocin aiki, da babura ga jami’an tsaro, da gina ofisoshin ƴansanda, da kuma taimakawa hukumomin DSS, da NSCDC, da Immigration ta hanyar kawo cibiyoyin horo a Gwarzo, da Kabo da Bichi.

ADVERTISEMENT

Ya ƙara da cewa fitilun tituna na Sola da ya saka a ƙananan hukumomin Kano Arewa da sauran yankuna ya taimaka wajen inganta aikin ƴan sintiri da rage laifuka. A cewarsa, irin waɗannan aiyuka su ne ya kamata gwamnatin jihar ta na yi, maimakon neman ɓata masa suna. Ya buƙaci gwamnatin Kano da ta yi koyi da irin wannan jajircewa wajen tabbatar da tsaro da ingantaccen mulki ga al’ummar jihar.

Barau
Abubakar Sulaiman
Website |  + postsBio
  • Abubakar Sulaiman
    Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 2, Sun Yi Garkuwa Da 30 A Kogi
  • Abubakar Sulaiman
    Gwamnatina Za Ta Mayar Da Hankali Kan Buƙatun Al’ummar Nasarawa – Wadada
  • Abubakar Sulaiman
    Ƴan Bindiga Sun Kai Hari Masallaci, Sun Kashe Wani Yaro A Kaduna
  • Abubakar Sulaiman
    Babachir Lawal Ya Fice Daga ADC, Ya Zargi Atiku Da Murɗe Zaben Fidda Gwani

MASU ALAKA

Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe
Siyasa

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
‘Yan Majalisar Wakilai 6 Daga Oyo Sun Fice Daga PDP Zuwa APM
Siyasa

‘Yan Majalisar Wakilai 6 Daga Oyo Sun Fice Daga PDP Zuwa APM

June 3, 2026
Gwamnatina Za Ta Mayar Da Hankali Kan Buƙatun Al’ummar Nasarawa – Wadada
Siyasa

Gwamnatina Za Ta Mayar Da Hankali Kan Buƙatun Al’ummar Nasarawa – Wadada

June 1, 2026
Next Post
Cutar Sikila Ba Mutuwa Ba Ce – Ƙwararru

Cutar Sikila Ba Mutuwa Ba Ce - Ƙwararru

LABARAI MASU NASABA

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

June 3, 2026
Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

June 3, 2026
Hada Kai Da ’Yan Awaren Yankin Taiwan Ba Zai Haifar Da Ɗa Mai Ido Ba

Hada Kai Da ’Yan Awaren Yankin Taiwan Ba Zai Haifar Da Ɗa Mai Ido Ba

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.