• English
  • Business News
Wednesday, August 27, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Shawarwarin Dattawan Arewa Kan Zaben 2023

by Yusuf Shuaibu
3 years ago
in Tambarin Dimokuradiyya
0
Shawarwarin Dattawan Arewa Kan Zaben 2023
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Kungiyar tuntuba na dattawan arewa (ACF) ta shawarci ‘yan Nijeriya su amince da duk wani sakamakon zaben wannan shekara domin farfado da dimokuradiyyar Nijeriya.

A cewar kungiyar, dole ne a samu wadanda suka yi nasara da kuma wadanda suka fadi, inda ta jaddada cewa ko ta yaya aka bi, ka da wani ya yi yunkurin rashin tayar da zaune tsaye ta hanyar tayar da hankulan ‘yan Nijeriya da sakamakon zaben.

  • Sin Za Ta Ci Gaba Da Taka Muhimmiyar Rawa Wajen Warware Rikici Cikin Lumana Ta Hanyarta
  • Sin Ta Yi Kira Ga Al’ummar Kasa Da Kasa Da Ta Kara Mai Da Hankali Kan Batun Somaliya

A wata sanarwa da babban sakataren kungiyar, Malam Murtala Aliyu ya fitar, ta ce duk wani yunkuri na kin amincewa da sakamakon zaben, zai zama wani mummunan farmaki ga dimokuradiyyar kasar nan, amincewa da zaben yana daya daga cikin ginshiki na tsarin dimokuradiyya.

Sanarwar ta bayyana cewa, “Kudirin ‘yan Nijeriya na kammala zaben 2023 cikin nasara bai taba shiga cikin shakku ba. Idan aka yi la’akari da duk abin da aka cimma, babu wani dalili da zai sa wani ya yi yunkurin yin kutse ga jadawalin zabe da aka sanar. Wannan ba zai zama abin karba kwata-kwata ba.”

Kungiyar dattawan arewa ta bukaci shugabanni a dukkan matakai da su dauki matakan tabbatar da tsaron rayuka da dukiyoyin daukacin ‘yan kasa da na kasashen waje a yankunansu gabanin zabe da lokacin zabe da kuma bayan zabe, inda ta ce ‘yan Nijeriya su tabbatar da an samu zaman lafiya da lumana daga gwamnatin farar hula zuwa wata gwamnatin ta farar huda.

Labarai Masu Nasaba

Zaben Cike Gurbi: Tinubu Ya Lalata Tsarin Zaben Nijeriya — ADC

An Samu Rarrabuwar Kawuna A Jam’iyyar ADC Kan Shugabancin David Mark

Haka kuma kungiyar ta shawarci kafafen yada labarai da su taka rawar gani wajen kawar da duk wani tashin hankali da ka iya tasowa lokacin bayyana sakamakon zabe.

ACF ta bayyana farin cikinta da bullo da fasahar sadarwa a harkar zabe, inda ta jaddada cewa mataki ne da ya dace da zai tabbatar da magance magudin zabe da aka saba a baya da kwace akwatin zabe da kuma sauya sakamakon zabe.

Kungiyar ta yi imanin cewa watsa sakamakon zabe ta yanar gizo daga wuraren zabe zuwa cibiyoyin tattara sakamakon zabe da kuma samar da kayayyakin da mutane za su rika sanya ido kan sakamakon zabe ta yanar gizo abubuwa ne da za su tabbatar da cewa ba a tafka magudi a zaben ba.

Sanarwar ta yaba wa kokarin Hukumar Zabe Mai Zaman Kanta ta Kasa (INEC) na samar da yanayi mai kyau da zai tabbatar da an gudanar da zabe cikin gaskiya da adalci, kuma duk kuri’un da aka kada a kasar nan za a kirga.

Kungiyar ta shawarci masu kada kuri’a da su yi la’akari da bayyanannun manufofin jam’iyya da kuma halaye da tarihin ‘yan takara.

Ta shawarci ‘yan Nijeriya da su kada kuri’unsu bisa la’akari da kabilanci, addini ko yanki, inda ta jaddada cewa ya kamata su nemi shugabannin da suka fi dacewa da muradun kasar nan.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: ArewaNagartaZabe
ShareTweetSendShare
Previous Post

Yadda Zaben 2023 Zai Bambanta Da Sauran Zabukan Nijeriya

Next Post

Yanzu Satar Da Kuka Yi Ba Ta Da Amfani: Kwankwaso Ga Gwamnonin APC

Related

Zaben Cike Gurbi: Tinubu Ya Lalata Tsarin Zaben Nijeriya — ADC
Tambarin Dimokuradiyya

Zaben Cike Gurbi: Tinubu Ya Lalata Tsarin Zaben Nijeriya — ADC

4 days ago
An Samu Rarrabuwar Kawuna A Jam’iyyar ADC Kan Shugabancin David Mark
Tambarin Dimokuradiyya

An Samu Rarrabuwar Kawuna A Jam’iyyar ADC Kan Shugabancin David Mark

2 weeks ago
Muhimman Batutuwan Da Za Mu Yi La’akari Da Su Kafin Amincewa Da Bukatun Kirkirar Sabbin Jihohi — Majalisar Dattawa
Tambarin Dimokuradiyya

Muhimman Batutuwan Da Za Mu Yi La’akari Da Su Kafin Amincewa Da Bukatun Kirkirar Sabbin Jihohi — Majalisar Dattawa

2 weeks ago
2027: Atiku, Obi Da Amaechi Za Su Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Takarar Shugaban Kasa A ADC
Tambarin Dimokuradiyya

ADC Ga Tinubu: Ina Wutar Lantarki Ta Awa 24 Da Ka Yi Wa ‘Yan Nijeriya Alkawari?

1 month ago
Dalilin Da Ya Sa Har Yanzu Obi Da El-Rufai Ba Su Shiga ADC A Hukumance Ba — Kakakin Jam’iyyar 
Tambarin Dimokuradiyya

Dalilin Da Ya Sa Har Yanzu Obi Da El-Rufai Ba Su Shiga ADC A Hukumance Ba — Kakakin Jam’iyyar 

1 month ago
Jam’iyyar PDP Ta Janye Daga Shiga Zaɓen Ƙananan Hukumomi A Kebbi
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Masu Neman Takarar Shugaban Kasa A PDP Sun Kara Matsa Kaimi Bayan Ficewar Atiku

1 month ago
Next Post
Yanzu Satar Da Kuka Yi Ba Ta Da Amfani: Kwankwaso Ga Gwamnonin APC

Yanzu Satar Da Kuka Yi Ba Ta Da Amfani: Kwankwaso Ga Gwamnonin APC

LABARAI MASU NASABA

Sin Da Kasashen Afirka Za Su Rubuta Sabon Babin Hakkin Dan Adam Bisa Ci Gabansu

Sin Da Kasashen Afirka Za Su Rubuta Sabon Babin Hakkin Dan Adam Bisa Ci Gabansu

August 27, 2025
Gwamnatin Imo Ta Amince Da N104,000 A Matsayin Sabon Mafi Ƙarancin Albashin Ma’aikata 

Gwamnatin Imo Ta Amince Da N104,000 A Matsayin Sabon Mafi Ƙarancin Albashin Ma’aikata 

August 27, 2025
Mazauna Kuyello A Jihar Kaduna Na Cikin Zullumin Bayyanar ‘Yan Ta’addar Ansaru

‘Yan Bindiga Sun Kashe Mutane 8 A Kaduna, Sun Jikkata Wasu

August 27, 2025
An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba

‘Yansanda Sun Ceto Mutum 5 Da Aka Sace A Jihar Kebbi

August 27, 2025
Jirgin Ƙasan Abuja-Kaduna Ya Yi Hatsari, Ba A San Halin Da Fasinjoji Ke Ciki Ba

NRC Ta Dakatar Da Sufurin Jirgin Ƙasan Abuja-Kaduna Bayan Hatsarin Da Ya Yi 

August 27, 2025
PDP Na Tattaunawa Da Obi Da Jonathan Kan Yi Mata Takarar Shugaban Ƙasa A 2027 – Moro

PDP Na Tattaunawa Da Obi Da Jonathan Kan Yi Mata Takarar Shugaban Ƙasa A 2027 – Moro

August 27, 2025
Kwalara Ta Kashe Mutum 7 A Zamfara, Sama Da Mutum 200 Sun Kamu Da Cutar

Kwalara Ta Kashe Mutum 7 A Zamfara, Sama Da Mutum 200 Sun Kamu Da Cutar

August 27, 2025
Gwamnati Ta Fara Aikin Gyara Na’urar Watsa Shirye-shirye Mai Gajeren Zango Ta Gidan Rediyon Muryar Nijeriya

Gwamnati Ta Fara Aikin Gyara Na’urar Watsa Shirye-shirye Mai Gajeren Zango Ta Gidan Rediyon Muryar Nijeriya

August 26, 2025
Shin Mummunan Halin Da Aka Shiga Yayin Yakin Duniya Na II Bai Isa Darasi Ba?

Shin Mummunan Halin Da Aka Shiga Yayin Yakin Duniya Na II Bai Isa Darasi Ba?

August 26, 2025
Gwamna Buni Ya Kaddamar Da Dashen Bishiyoyi Na 2025

Gwamna Buni Ya Kaddamar Da Dashen Bishiyoyi Na 2025

August 26, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.