• English
  • Business News
Sunday, June 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Hajjin 2023: Miliyan 3 Kowane Maniyyaci Zai Biya A Bana —NAHCON

by Abubakar Abba
2 years ago
in Manyan Labarai
0
Hajjin 2023: Miliyan 3 Kowane Maniyyaci Zai Biya A Bana —NAHCON
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Hukumar Jin Dadin Alhazai ta Kasa (NAHCON), ta ce kowane maniyyaci da zai je aikin Hajjin 2003, zai biya Naira miliyan 2.89.

Shugaban hukumar na kasa, Zikrullah Hassan ne, ya sanar da hakan a yau Juma’a, inda ya danganta hakan da hauhawar farashin kaya a Nijeriya da kuma Saudiyya.

  • An Samu Tsohuwar Hedimasta Da Laifin Yi Wa Dalibai Fyade
  • Buhari Ya Gaza Gudanar Da Sahihin Zabe A 2023 – Kwankwaso

Hassan, ya ce an tsara farashin bisa kashi takwas, inda jihohin Borno da Yobe, ke da karancin farashi sai kuma jihohin Legas da Ogun na su farashin ya fi yawa, wanda ya kai Naira miliyan 2.99.

Rahotannin sun bayyana cewa, karin kudin hajjin ya kai sama da Naira 300,000, inda aka kwatanta da kudin da alhasai suka biya a 2022.

Ya kara da cewa, farashin aikin hajjin, tsadarsa kashi takwas ne, inda maniyyacin da ya fito daga Maiduguri da wanda ya fito daga Yola, kowanensu zai biya Naira miliyan 2.89 sauran wadanda suka fito daga jihohin Arewa kuwa, kowane maniyyaci zai biya Naira miliyan 2.919.

Labarai Masu Nasaba

Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya

Gobara Ta Ƙone Wani Sashe Na Kasuwar Waya A Kano

A cewarsa, kudancin kasar kuwa, na da farashin kashi shida, inda Jihar Edo da sauran jihohin da ke a Kudu maso Kudu da kuma a Kudu maso Gabas kowane maniyyaci zai biya Naira miliyan 2.9, inda kuma wadanda suka fito daga jihohin Ekiti da Ondo, kowane zai biya Naira miliyan 2.88.

Kazalika, ya ce kowane maniyyaci daya da ya fito daga Jihar Osun, zai biya Naira miliyan 2.99, inda maniyyaci daya da ya fito daga Jihar Kuros Ribas zai biya Naira miliyan 2.943, haka kowane maniyyacin daya da ya fito daga jihar Legas, Ogun da Oyo, zai biya Naira miliyan 2.99.

Ya ce an samu bambamcin farashin ne domin jihohin da ke Arewa sun fi makwabtaka da Saudiyya fiye da sauran jihohin da ke a kudancin kasar nan, inda kuma masaukan maniyyatan da kowace jiha za ta kama ke nuna abin da ya kamata maniyyaci zai biya.

Bugu da kari, kamfanonin jiragen saman da aka sahale wa su yi jigilar maniyyatan zuwa kasar mai tsarki su ne; Air Peace, Azman Air, Fly Nas, Aero Contractors da kuma Max Air, inda Arik Air da kuma Value jet.

Shugaban, ya ce za rufe rumbun adana bayanan hukumar ga wadanda suka yi zabi su shiga shirin zuwa kasar mai tsarki ta hanyar zuba kudin adashin gata a ranar 21 ga watan Afirilu, 2023.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Aikin HajjiHajjin BanaJiragen SamaKarin FarashiMiliyan 3NAHCONSaudiyaTsada
ShareTweetSendShare
Previous Post

GORON JUMA’A

Next Post

Za A Yi Mukabala Da Sheikh Idris A Bauchi Kan Kalamansa Game Da Manzon Allah SAW 

Related

Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya
Manyan Labarai

Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya

17 hours ago
Gobara Ta Ƙone Wani Sashe Na Kasuwar Waya A Kano
Manyan Labarai

Gobara Ta Ƙone Wani Sashe Na Kasuwar Waya A Kano

1 day ago
Sarki Sanusi II Ya Soke Hawan Sallah, Ya Bayyana Dalili
Manyan Labarai

Sarki Sanusi II Ya Soke Hawan Sallah, Ya Bayyana Dalili

2 days ago
Saƙon Barka Da Sallah: Tinubu Ya Baiyana Tabbacin Ci Gaban Nijeriya, Da Sauyin Tattalin Arziƙi
Manyan Labarai

Saƙon Barka Da Sallah: Tinubu Ya Baiyana Tabbacin Ci Gaban Nijeriya, Da Sauyin Tattalin Arziƙi

2 days ago
Abubuwan Da Ba A Fada Ba Game Da Mummunar Ambaliyar Ruwan Mokwa
Manyan Labarai

Abubuwan Da Ba A Fada Ba Game Da Mummunar Ambaliyar Ruwan Mokwa

2 days ago
Hukumar kashe gobara
Manyan Labarai

An Samu Asarar Dukiya ta Miliyan ₦273, Tare Da Mutuwar Mutum 5 A Kano – Hukuma

2 days ago
Next Post
Za A Yi Mukabala Da Sheikh Idris A Bauchi Kan Kalamansa Game Da Manzon Allah SAW 

Za A Yi Mukabala Da Sheikh Idris A Bauchi Kan Kalamansa Game Da Manzon Allah SAW 

LABARAI MASU NASABA

Tattaunawar Da Shugabannin Sin Da Amurka Suka Yi Ta Wayar Tarho Ta Ba Da Jagoranci Ga Dangantakar Dake Tsakanin Kasashen Biyu

Tattaunawar Da Shugabannin Sin Da Amurka Suka Yi Ta Wayar Tarho Ta Ba Da Jagoranci Ga Dangantakar Dake Tsakanin Kasashen Biyu

June 7, 2025
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi

An Kama Magidanci A Bauchi Bisa Zargin Lalata Da Agolarsa

June 7, 2025
Dabarar Yaudara Ta Kasar Philippines Kan Batun Tekun Kudancin Sin Ta Fito Fili

Dabarar Yaudara Ta Kasar Philippines Kan Batun Tekun Kudancin Sin Ta Fito Fili

June 7, 2025
Wang Yi Ya Nanata Matsayin Taiwan Yayin Tattaunawa Da Takwaransa Na Faransa

Wang Yi Ya Nanata Matsayin Taiwan Yayin Tattaunawa Da Takwaransa Na Faransa

June 7, 2025
Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote

Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote

June 7, 2025
Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne

Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne

June 7, 2025
Hukumar NPA Ta Bayar Da Kwangilar Aikin Ruwa Na Tashar Lekki

Hukumar NPA Ta Bayar Da Kwangilar Aikin Ruwa Na Tashar Lekki

June 7, 2025
Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya

Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya

June 7, 2025
Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su

Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su

June 7, 2025
Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

June 7, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.