• English
  • Business News
Friday, August 22, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Musabbabin Haramta Sana’ar Gwangwan A Jihar Borno

by Muhammad Maitela
2 years ago
in Tambarin Dimokuradiyya, Rahotonni
0
Musabbabin Haramta Sana’ar Gwangwan A Jihar Borno
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A kokarin dakile yawan kai wa masu sana’ar tsoffin karafa farmakin da mayakan Boko Haram ke yi a jihar Borno, Gwamna Farfesa Babagana Zulum, ya kafa dokar haramta sana’ar a fadin jihar, har sai baba ta gani.

Gwamnatin jihar ta kara da cewa, kafa dokar ya zama dole domin kare rayukan masu sana’ar gwangwan, sakamakon hare-haren da `yan ta’addan Boko Haram ke kai musu a baya-bayan nan.

  • Cire Tallafin Mai: Za A Kara Farashin Burodi A Nijeriya
  • Kyakkyawar Alakar Sin Da Amurka Fa’ida ce Ga Duniya Baki Daya

A wata sanarwar manema labaru mai dauke da sa-hannun Mallam Isa Gusau, mai magana da yawun Gwamna Zulum, ya ce, “An kafa wannan dokar ce domin dakile farmakin da yan ta’addan Boko Haram ke kai wa masu wannan sana’ar a wasu kananan hukumomi da kuma hana satar dukiyar jama’a da ake yawan samu.”

Gusau ya kara da cewa, hakan ya zo ne sakamakon yadda wasu wadanda ba a san ko su waye ba, suna zuwa kauyukan da yan ta’addan Boko Haram suka tarwatsa, domin neman tsoffin karafa, inda Boko Haram ke yi musu kwanton bauna tare da kashe su.”

A cewar Gwamna Zulum “A cikin shekaru biyar da suka wuce, an kashe mutane da dama a lokacin da suke shiga kauyuka, a sana’ar gwangwan. Hakan ya sanya dole gwamnatin jihar Borno ta dauki matakin bincike kan matsalolin, al’amarin da ya tilasta kafa wannan dokar.” In ji Zulum.

Labarai Masu Nasaba

Dambarwar 2027 Da Kalubalen Da Ke Gaban Jam’iyyun Siyasa

An Samu Rarrabuwar Kawuna A Jam’iyyar ADC Kan Shugabancin David Mark

“Sannan kuma a wadannan wuraren, akwai dukiyoyin gwamnati, da na kamfanonin sadarwa. Wanda irin wadannan ayyuka na sana’ar gwangwan ke zama kalubale da kuma zagon kasa ga Gwamnatin Tarayya da na jihar Borno wajen kula da su. Saboda haka na bayar da umarnin hana sana’ar gwangwan ta karafa a dukkan kananan hukumomin jihar Borno 27.”

Bugu da kari, Gwamna Zulum ya bayyana cewa, wadannan masu sana’ar gwangwan sun yi kaurin suna wajen lalata dukiyoyin jama’a da na kamfanoni masu zaman kansu a mafi yawan kananan hukumomin da rikicin Boko Haram ya tilasta wa mazaunansu tserewa.

Gwamna Zulum ya kara da cewa gwamnatin jihar ta yi asarar kadarori na biliyoyin Naira a cikin shekaru biyar da suka gabata sakamakon ayyukan masu sana’ar gwangwan a jihar.

Gwamnan ya ce wannan dokar ta shafi duk wani nau’i na sana’ar tsoffin karafa wanda ba bisa ka’ida ba, wanda ya hada da wargazawa, tarawa, da kuma jigilar tsoffin karafan a fadin jihar.

Gwamna Zulum ya yi gargadin cewa gwamnatin jihar Borno za ta hada gwiwa da jami’an tsaro wajen aiwatar da dokar yadda ya kamata tare da zartar da hukunci mai tsauri ga duk wanda ya karya dokar.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: BornoMaiduguriSana'ar GwangwanZulum
ShareTweetSendShare
Previous Post

Ribadu Zai Shugabanci Taron LEADERSHIP Da NDLEA Kan Yaki Da Miyagun Kwayoyi

Next Post

Daidaita Farashin Canji Ya Fara Haifar Da Da Mai Ido A Nijeriya

Related

Dambarwar 2027 Da Kalubalen Da Ke Gaban Jam’iyyun Siyasa
Rahotonni

Dambarwar 2027 Da Kalubalen Da Ke Gaban Jam’iyyun Siyasa

6 days ago
An Samu Rarrabuwar Kawuna A Jam’iyyar ADC Kan Shugabancin David Mark
Tambarin Dimokuradiyya

An Samu Rarrabuwar Kawuna A Jam’iyyar ADC Kan Shugabancin David Mark

1 week ago
Muhimman Batutuwan Da Za Mu Yi La’akari Da Su Kafin Amincewa Da Bukatun Kirkirar Sabbin Jihohi — Majalisar Dattawa
Tambarin Dimokuradiyya

Muhimman Batutuwan Da Za Mu Yi La’akari Da Su Kafin Amincewa Da Bukatun Kirkirar Sabbin Jihohi — Majalisar Dattawa

1 week ago
Rawar Da Dakta Bello Matawalle Ke Takawa Wajen Inganta Harkokin Tsaro A Nijeriya
Rahotonni

Rawar Da Dakta Bello Matawalle Ke Takawa Wajen Inganta Harkokin Tsaro A Nijeriya

1 week ago
Tinubu Ya Yi Wa Arewa Kokari Fiye Da Duk Wani Shugaba A Tarihin Nijeriya -Kwamared Dauda
Rahotonni

Tinubu Ya Yi Wa Arewa Kokari Fiye Da Duk Wani Shugaba A Tarihin Nijeriya -Kwamared Dauda

1 week ago
Yadda Masu Bukata Ta Musamman Suka Rungumi Sabbin Dabarun Noma Domin Ciyar Da Kansu
Rahotonni

Yadda Masu Bukata Ta Musamman Suka Rungumi Sabbin Dabarun Noma Domin Ciyar Da Kansu

4 weeks ago
Next Post
Daidaita Farashin Canji Ya Fara Haifar Da Da Mai Ido A Nijeriya

Daidaita Farashin Canji Ya Fara Haifar Da Da Mai Ido A Nijeriya

LABARAI MASU NASABA

Wajibi Ne Sassan Kasa Da Kasa Su Raya Ruhin Jin Kan Bil’adama

Wajibi Ne Sassan Kasa Da Kasa Su Raya Ruhin Jin Kan Bil’adama

August 22, 2025
UNICEF Na Neman Naira Biliyan 240 Don Ayyukan Agaji A Nijeriya

UNICEF Na Neman Naira Biliyan 240 Don Ayyukan Agaji A Nijeriya

August 22, 2025
Sin Ta Samu Karin Kamfanoni Kusan Miliyan 20 A Cikin Shirin Shekaru Biyar Karo Na 14

Sin Ta Samu Karin Kamfanoni Kusan Miliyan 20 A Cikin Shirin Shekaru Biyar Karo Na 14

August 22, 2025
Ɓarayin Waya Sun Hallaka Ɗalibin ATAP A Bauchi

Ɓarayin Waya Sun Hallaka Ɗalibin ATAP A Bauchi

August 22, 2025
JAMB Ta Kaddamar Da Kwamitin Bincike Kan Satar Jarabawa

JAMB Ta Kaddamar Da Kwamitin Bincike Kan Satar Jarabawa

August 22, 2025
Wadanda Suka Mutu A Wani Hadarin Ginin Gada A Sin Sun Karu Zuwa 12

Wadanda Suka Mutu A Wani Hadarin Ginin Gada A Sin Sun Karu Zuwa 12

August 22, 2025
Raguwar Hauhawar Farashi: ‘Yan Nijeriya Da ‘Yan Kasuwa Ba Su Ga Saukin A Zahirance Ba

Raguwar Hauhawar Farashi: ‘Yan Nijeriya Da ‘Yan Kasuwa Ba Su Ga Saukin A Zahirance Ba

August 22, 2025
Kamfanin Novo Nordisk Na Denmark Zai Ci Gaba Da Zuba Jari A Kasar Sin A Bana

Kamfanin Novo Nordisk Na Denmark Zai Ci Gaba Da Zuba Jari A Kasar Sin A Bana

August 22, 2025
Xi Jinping Zai Halarci Taron Kolin SCO Na 2025

Xi Jinping Zai Halarci Taron Kolin SCO Na 2025

August 22, 2025
Ruben Dias Ya Rattaba Hannu Kan Sabon Kwantiragi A Manchester City

Ruben Dias Ya Rattaba Hannu Kan Sabon Kwantiragi A Manchester City

August 22, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.