• English
  • Business News
Sunday, June 29, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

‘Yan Nijeriya Sun Fara Nadamar Zaben Tinubu – Shugaban PDP Na Ondo

by Yusuf Shuaibu
2 years ago
in Tambarin Dimokuradiyya
0
‘Yan Nijeriya Sun Fara Nadamar Zaben Tinubu – Shugaban PDP Na Ondo
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Babbar jam’iyyar adawa ta PDP ta bayyana cewa a yanzu haka ‘yan Nijeriya wadanda suka zabi Shugaban Kasa, Bola Ahmed Tinubu suna nadama.

Shugaban jam’iyyar PDP a Jihar Ondo, Fatai Adams, ya bayyana hakan ne a wata sanarwa dauke da sa hannun sakataren yada labaran jam’iyyar, Kennedy Peretei da ya fitar birnin Akure.

  • Muna Bibiyar Masu Juyin Mulkin Nijar, Mu Ga Iya Gudun Ruwansu – Tinubu

A cewar jam’iyyar, ‘yan watannin da shugaban ya yi a kan karagar mulki ya kara ingiza ‘yan Nijeriya a cikin mawuyacin hali na tsadar rayuwa da ba a taba ganin irinsa ba.

Adams wanda ke mayar da martani ga shugaban jam’iyyar APC mai mulki a Jihar Ondo, Ade Adetimehin, wanda ya ce jam’iyyar PDP ta fada cikin rudani.

Ya ce a maimakon jam’iyyar APC da gwamnatinta su mayar da hankali kan mawuyacin halin da suka jefa ‘yan Nijeriya a ciki na tsawaon shakara 8 da suka yi a kan karagar mulki, sai suka kama wani abu daban.

Labarai Masu Nasaba

Cacar Baki Ta Kaure Tsakanin Fadar Shugaban Kasa Da Peter Obi Kan Tallafin Mai

Sauya Sheka Ya Sa APC Ta Samu Gagarumin Rinjaye A Majalisun Tarayya

A cewarsa, “Kila Adetimehin shi ne kadai mutumin da ya manta da cewa, al’ummar Jihar Ondo suna sane cewa jam’iyyarsa ta APC ita ce silar da ta jefa mutane cikin wannan mawuyacin halin da suke ciki a halin yanzu, musamman ma lokacin da aka cire tallafin mai.

“Bai fahimci lamarin ba, wanda hatta wadanda aka yaudare su su zabi APC a 2023, tuni sun yi nadama tare da kokawa da yadda kuskuransu suka jawo wa kansu da iyalansu wahala.

“Irin wannan mutum idan yana da kunya ya kamata ya durkusa ya roki al’umma kan babbar masifar da jam’iyyarsa ta jefa mutane.

“Har yana iya bude bakinsa ya ce PDP ta mutu, wannan ai abun dariya ne.
Da yake mayar da martani game da sauya shekar ‘ya’yan PDP zuwa jam’iyya mai mulki a jihar, Adams ya ce “Mafi rinjayen kansilolin 203 da Adetimehin ke bikin shiga jam’iyyarsa ba su taka rawar gani ba a zabukan da suka gabata a Jihar Ondo.

“Kadan daga cikinsu sun kasance a APC tun 2016. A bayyana yake yadda suka sauya sheka zuwa PDP haka suka koma APC, amma ba kowa ne zai iya fahimtar ba, musamman Adetimehin da ke shugabantar jam’iyyar APC mai cike da hadari a jihar, ya kamata ya daina yaudarar kansa.

“Jam’iyyar PDP a Jihar Ondo ta rabauta da wasu ‘yan tsiraru da ke cikin halin kaka-ni-ka-yi a cikin jirgin Adetimehin na APC da ya nutse.

“Yayin da muke tausaya wa irin wadannan mutane, abin takaici ne wadanda ya kamata su yi kuka suna rawa da murna.
“Amma ba da dadewa ba, gaskiyar za ta bayyana a kansu cewa lalle sun kasance makarya”.

Shugaban jam’iyyar ya bayyana cewa PDP ba ta durkushe ba, kuma hakan ba zai taba faruwa ba.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: APCPDP
ShareTweetSendShare
Previous Post

Taron Kolin BRICS Zai Ingiza Daidaito Da Karsashi Ga Duniya Mai Cike Da Tashin Tashina

Next Post

Abba Da Ganduje Sun Yi Ta’aziyyar Rasuwar Abdullahi Yakubu Wakilin Jaridar Leadership Na Kano

Related

Cacar Baki Ta Kaure Tsakanin Fadar Shugaban Kasa Da Peter Obi Kan Tallafin Mai
Tambarin Dimokuradiyya

Cacar Baki Ta Kaure Tsakanin Fadar Shugaban Kasa Da Peter Obi Kan Tallafin Mai

2 weeks ago
APC
Tambarin Dimokuradiyya

Sauya Sheka Ya Sa APC Ta Samu Gagarumin Rinjaye A Majalisun Tarayya

2 weeks ago
Adawa
Tambarin Dimokuradiyya

Yadda Rarrabuwar Kawunan Jam’iyyu Zai Iya Sauya Alkiblar Zaben 2027

3 weeks ago
‘Yancin Kananan Hukumomi: Shekara Daya Da Hukuncin Kotun Koli Amma Ba A Aiwatar Ba
Tambarin Dimokuradiyya

‘Yancin Kananan Hukumomi: Shekara Daya Da Hukuncin Kotun Koli Amma Ba A Aiwatar Ba

4 weeks ago
Ko Kwamitin Saraki Zai Iya Ceto PDP Daga Rikicin Cikin Gida?
Tambarin Dimokuradiyya

Ko Kwamitin Saraki Zai Iya Ceto PDP Daga Rikicin Cikin Gida?

1 month ago
Tsadar Rayuwa Da Karuwar Ta’addanci Na Ci Gaba Da Tagayyara ‘Yan Nijeriya
Tambarin Dimokuradiyya

‘Yan Adawa Na Cacakar APC A Yankin Arewa Maso Yamma Bisa Goyon Bayan Tazarcen Tinubu

1 month ago
Next Post
Abba Da Ganduje Sun Yi Ta’aziyyar Rasuwar Abdullahi Yakubu Wakilin Jaridar Leadership Na Kano

Abba Da Ganduje Sun Yi Ta'aziyyar Rasuwar Abdullahi Yakubu Wakilin Jaridar Leadership Na Kano

LABARAI MASU NASABA

Babbar Mota Ta Afka Cikin Kasuwa A Taraba, Mutane Da Yawa Sun Mutu

Babbar Mota Ta Afka Cikin Kasuwa A Taraba, Mutane Da Yawa Sun Mutu

June 29, 2025
Shugaban Majalisar Dokokin Jama’ar Kasar Mexico: Tunanin Raya Al’umma Mai Kyakkyawar Makoma Ga Dukkan Bil’adama Da Shugaba Xi Jinping Ya Gabatar Ya Kayatar

Shugaban Majalisar Dokokin Jama’ar Kasar Mexico: Tunanin Raya Al’umma Mai Kyakkyawar Makoma Ga Dukkan Bil’adama Da Shugaba Xi Jinping Ya Gabatar Ya Kayatar

June 29, 2025
Sin Na Adawa Da Duk Wata Yarjejeniyar Haraji Da Ka Iya Illata Moriyarta

Sin Na Adawa Da Duk Wata Yarjejeniyar Haraji Da Ka Iya Illata Moriyarta

June 29, 2025
2027: Ƴan Adawa Na Ƙara Ƙaimin Kawar Da Tinubu

2027: Ƴan Adawa Na Ƙara Ƙaimin Kawar Da Tinubu

June 29, 2025
Yadda Yaƙin Iran Da Isra’ila Zai Iya Shafar Zamantakewa Da Tattalin Arziƙin Nijeriya

Yadda Yaƙin Iran Da Isra’ila Zai Iya Shafar Zamantakewa Da Tattalin Arziƙin Nijeriya

June 29, 2025
Ƙwallon Mata: Rivers United Ta Doke Nasarawa Amazons A Wasan Ƙarshe Na Kofin Shugaban Ƙasa

Ƙwallon Mata: Rivers United Ta Doke Nasarawa Amazons A Wasan Ƙarshe Na Kofin Shugaban Ƙasa

June 29, 2025
Xi Ya Yi Kira Ga Mazauna Wani Kauye Dake Xizang Da Su Rike ‘Yan Uwantakar Kabila

Xi Ya Yi Kira Ga Mazauna Wani Kauye Dake Xizang Da Su Rike ‘Yan Uwantakar Kabila

June 29, 2025
Zaben 2027 Yaƙi Ne Tsakanin Talakawa Da Masu Mulki – Sanata Kaita 

Zaben 2027 Yaƙi Ne Tsakanin Talakawa Da Masu Mulki – Sanata Kaita 

June 29, 2025
Gyaran Tsarin Mulki: Majalisa Ta Shirya Sauraron Jin Ra’ayoyin Jama’a A Wasu Sassan Nijeriya

Gyaran Tsarin Mulki: Majalisa Ta Shirya Sauraron Jin Ra’ayoyin Jama’a A Wasu Sassan Nijeriya

June 29, 2025
Yara 150,000 Ake Haifa Da Cutar Sikila A Nijeriya Duk Shekara – Rahoto

Yara 150,000 Ake Haifa Da Cutar Sikila A Nijeriya Duk Shekara – Rahoto

June 29, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.