• English
  • Business News
Saturday, June 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kalubalen Da Zaben Gwamnonin Imo, Kogi Da Bayelsa Ke Fuskanta

by Yusuf Shuaibu
2 years ago
in Tambarin Dimokuradiyya
0
Kalubalen Da Zaben Gwamnonin Imo, Kogi Da Bayelsa Ke Fuskanta
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Kwanaki kadan ya rage a gudanar da zaben gwamna a jihohin Kogi, Imo da Bayelsa, sai dai akwai wasu kalubale da zabukan ka iya fuskanta, musamman na rashin tsaro da kaurace wa zaben da kuma yadda hukumar zabe mai zaman kanta za ta iya gudanar da sahihin zabe a daukacin jihohin ba tare da wata matsala ba.

Shi ya sa ma, tsohon shugaban kasa, Abdulsalami Abubakar da, Rabaran Mathew Hassan Kukah, sun yi kira ga daukacin ‘yan takara da magoya baya da su yi kokarin wajen gudanar da zabukan ba tare da tashe-tashen hankula ba.

Wannan dai na zuwa ne a daidai lokacin da manyan ‘yan takarar gwamna a jihohin suke cacar baki tare da sukar juna, wanda hakan na iya haddasa tashe-tashen hankula a jihohinsu.

A yayin da zaben gwamna a jihohin uku zai gudana a ranar 11 ga watan Nuwamba, 2023, kwamitin zaman lafiya na kasa karkashin jagorancin Abdulsalami da Kukah ya damu matuka kan zaman lafiya da tsaro a jihohin, kuma ya bukaci ‘yan takarar su rattaba hannu kan yarjejeniyar zaman lafiya.
Akwai fargaba dangane kan dalilin da suka sa ake ci gaba da samun tashe-tashen hankula a lokacin zabe a Nijeriya duk da kokarin da hukumoma da sauran masu ruwa da tsaki ke yi.

A saboda haka, kwamitin zaman lafiya na kasa ya ce ba zai karaya ba har sai halayen wasu ‘yan siyasa sun sauya a lokacin zabe, inda ya dage cewa zai yi kokarin ganin an gudanar da zaben cikin zaman lafiya bisa jajircewar ‘yan takarar gwamna da jam’iyyunsu da sauran masu ruwa da tsaki.

Labarai Masu Nasaba

Yadda Rarrabuwar Kawunan Jam’iyyu Zai Iya Sauya Alkiblar Zaben 2027

‘Yancin Kananan Hukumomi: Shekara Daya Da Hukuncin Kotun Koli Amma Ba A Aiwatar Ba

A Jihar Imo
Da yake tofa albarkacin bakinsa, dan takarar gwamnan Jihar Imo a karkashin jam’iyyar PDP, Sanata Samuel Anyanwu, ya ce matakin da gwamnatin jihar take dauka na tunkarar kalubalen tsaro ne ke haddasa tashe-tashen hankula a jihar.

Anyanwu ya ce matasan jihar ba su da aikin yi, inda ya shawarci gwamnati da ta samar da ayyukan yi da gina masana’antu da samar da yanayin da zai taimaka wajen bunkasa kasuwanci.

A cewarsa, hakkin gwamnati ne ta kare rayuka da dukiyoyin al’umma, ya idan gwamnati ta kasa haka, za a kira ta da sunan wacce ta gaza.

A nasa bangaren, dan takarar gwamna na jam’iyyar LP, Sanata Athan Achonu ya kuma zargi gwamnatin jihar kan rashin tsaro a jihar.

‘Yan takarar sun nuna cewa a shirye suke su rattaba hannu kan yarjejeniyar zaman lafiya da kuma kudurin gudanar da zabe ba tare da tashin hankali ba.

Sai dai kuma, gwamnan jihar kuma dan takara a karkashin jam’iyyar APC, Hope Uzodimma y ace gwamnatinsa tana kokari wajen magance duk wani kalubalen da ka iya shafar zaben.

Kwamishiniyar zaben jihar, Farfesa Sylbia Agu ta bayyana cewa hukumar zaben ta yi isassun shirye-shirye tare da jami’an tsaro wajen kare ma’aikatanta.

A Jihar Kogi
A Jihar Kogi, dan takarar gwamna na jam’iyyar SDP, Murtala Ajaka, ya nuna sha’awarsa na sanya hannu kan duk wata yarjejeniyar zaman lafiya.

LEADERSHIP tuntubi mai magana da yawun kwamitin yakin neman zaben APC, Kingsley Fanwo da kuma babban mataimaki na musamman ga gwamnan Kogi kan harkokin yada labarai, Michael Ozigi, kan ko dan takararsu zai sanya hannu kan yarjejeniyar zaman lafiya, amma duk su biyun ba su amsa ba.

Haka shi ma, dan takarar jam’iyyar PDP, Dino Melaye bai amsa ba.

A Jihar Bayelsa
An kasa masun ‘yan takarar manyan jam’iyyun siyasa uku da mambobin majalisar yakin neman zabensu.

Hakan ya kasance ne sakamakon kara zafafa yakin neman zabe da jam’iyyu suke gudanarwa a dukkan kananan hukumomin jihar.

Dangane da matakan da hukumar zabe ke dauka na kare ma’aikatanta, shugaban sashen wayar da kan masu jefa kuri’a, Wilfred Ifogah, ya ce hukumar ta gudanar da tattaunawa da dama da masu ruwa da tsaki a harkar tsaro a zaben.

Ya ce, “INEC ba ta aiki ita kadai ba. Akwai kwamitin tuntuba tsakanin hukumomin tsaro kan harkokin zabe (ICCES). Wannan tawaga ce ta dukkan hukumomin tsaro da ake da su a zaben jihar. Kwamishinan zabe da kwamishinan ‘yansanda ne ke jagorantar tawagar a kwacce jiha.”

A cewarsa, duk wannan na faruwa ne domin tabbatar da cewa masu kada kuri’a za su kasance a rumfunan zabe ba tare da wata matsala ba.

Tuni dai ake ci gaba da samun rashin tsaro a wadannan jihohi da za a gudanar da zaben gwamna.

Yayin da zaben Kogi zai iya samun cikas da ayyukan ‘yan daba kamar yadda aka gani a zaben da ya gabata, masu zabe a Imo da jami’an INEC na iya samun kalubalan ‘yan bindiga.

Har ila yau, a Jihar Bayelsa lamarin na matukar tayar da hankali, inda wasu ‘yan bindiga da ake zargin makiyaya ne ke kai hare-hare kan manoma da fararen hula har ma da jami’an tsaro.

Ita ma hukumar zabe na iya samu matsaloli wajen gudanar da zaben, wadanda suka shafi kan kayan aiki a lungu da sako na jihohin da saka sakamakon zabe ta na’ura da dai sauransu.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Dino MelayeINECZabe
ShareTweetSendShare
Previous Post

Abun Da Ya Faru A MDD Gargadi Ne Ga Amurka

Next Post

Dalilan Mayar Da Daukaka Kararrakin Zabe 1,209 Zuwa Abuja Da Legas

Related

Adawa
Tambarin Dimokuradiyya

Yadda Rarrabuwar Kawunan Jam’iyyu Zai Iya Sauya Alkiblar Zaben 2027

12 hours ago
‘Yancin Kananan Hukumomi: Shekara Daya Da Hukuncin Kotun Koli Amma Ba A Aiwatar Ba
Tambarin Dimokuradiyya

‘Yancin Kananan Hukumomi: Shekara Daya Da Hukuncin Kotun Koli Amma Ba A Aiwatar Ba

1 week ago
Ko Kwamitin Saraki Zai Iya Ceto PDP Daga Rikicin Cikin Gida?
Tambarin Dimokuradiyya

Ko Kwamitin Saraki Zai Iya Ceto PDP Daga Rikicin Cikin Gida?

2 weeks ago
Tsadar Rayuwa Da Karuwar Ta’addanci Na Ci Gaba Da Tagayyara ‘Yan Nijeriya
Tambarin Dimokuradiyya

‘Yan Adawa Na Cacakar APC A Yankin Arewa Maso Yamma Bisa Goyon Bayan Tazarcen Tinubu

2 weeks ago
Shugaban INEC Ya Yi Kira Da A Sake Fasalin Tsarin Zabe Gabanin 2027
Tambarin Dimokuradiyya

Shugaban INEC Ya Yi Kira Da A Sake Fasalin Tsarin Zabe Gabanin 2027

1 month ago
Kogi
Tambarin Dimokuradiyya

Amfani Da Karfin Gwamnati Kan ‘Yan Adawa Zai Jawo Wa Tinubu Illa A 2027 – Sule Lamido

1 month ago
Next Post
Dalilan Mayar Da Daukaka Kararrakin Zabe 1,209 Zuwa Abuja Da Legas

Dalilan Mayar Da Daukaka Kararrakin Zabe 1,209 Zuwa Abuja Da Legas

LABARAI MASU NASABA

Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote

Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote

June 7, 2025
Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne

Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne

June 7, 2025
Hukumar NPA Ta Bayar Da Kwangilar Aikin Ruwa Na Tashar Lekki

Hukumar NPA Ta Bayar Da Kwangilar Aikin Ruwa Na Tashar Lekki

June 7, 2025
Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya

Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya

June 7, 2025
Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su

Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su

June 7, 2025
Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

June 7, 2025
Nazarin CGTN: Jama’ar Duniya Na Ganin Tattaunawa Da Hadin Gwiwa A Matsayin Hanyar Warware Takaddamar Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka

Nazarin CGTN: Jama’ar Duniya Na Ganin Tattaunawa Da Hadin Gwiwa A Matsayin Hanyar Warware Takaddamar Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka

June 7, 2025
Sojojin Sama Sun Tarwatsa Maɓoyar Ƴan Ta’adda, Ya Daƙile Hari Ranar Idi A Borno

Sojojin Sama Sun Tarwatsa Maɓoyar Ƴan Ta’adda, Ya Daƙile Hari Ranar Idi A Borno

June 7, 2025
Kogi

2027: An Yi Kira Ga Masu Mulki Da Su Rungumi Tafarkin Inganta Rayuwar Al’umma

June 7, 2025
Tottenham Ta Raba Gari Da Kocinta Ange Postecoglu

Tottenham Ta Raba Gari Da Kocinta Ange Postecoglu

June 7, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.