• English
  • Business News
Saturday, July 26, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Asalin Kungiyoyin Mayakan Hamas, Hizbullah Da Manufofinsu

by Sulaiman and Salim Sani Shehu
2 years ago
in Labarai
0
Asalin Kungiyoyin Mayakan Hamas, Hizbullah Da Manufofinsu
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Yayin da Isra’ila ke kai wa sojojin Hamas da Gaza hari ba ji ba gani, ana iya ganin irin yadda yakin ke ta’azzara da kuma yadda ake samun asarar rayuka musamman ma a Gaza. Amma Babbar barazana ga Isra’ila ita ce ta Hezbollah, kungiyar Mayaka ko kuma masu fafutukar siyasa da suke da yawa da kuma karfi a kasar Lebanon kuma su kai iyaka da Isra’ila ta Arewacin kasar.

Kungiyar mayakan Hamas da Hizbullah suna samun goyon bayan Iran, wanda kuma su dukkansu suna da buri da yunkurin ganin sun darkusar ko kwatar kansu daga Isra’ila.
Wannan matsayi suna daukarsa a matsayin babban muradinsu.

Duk kungiyoyin mayakan biyu suna da bambance-bambance irin nasu da kuma manufofin kafa su, wannan shi ne ya janyo rashin tasirin kungiyar mayakan Hezbollah kan yakin da kungiyar mayakan Hamas ke yi da Isra’ila.

Kungiyar Mayakan Hizbullah
Hizbullah wacce kalmar Larabci ce da ta ke nufin ” Kungiyar Allah “. Kungiyar tana daukar kanta a matsayin wani bangare na akidun Shi’a. Akidar Shi’a tai kaurin suna wajen da mayar da hankali kan kora tare da sukar Turawan Yamma da kuma masu mara mata baya irin su Amurka. Sannan tana cikin kasashen da suke gaba-gaba wajen kin amincewa da Isra’ila a matsayin kasa.

Tarihinsu
An kafa kungiyar ne a shekara ta 1982, lokacin da ake tsaka da yakin basasar Kasar Lebanon wanda aka shafe shekaru 15 ana yinsa. Bayan da Isra’ila ta mamaye Kasar Lebanon a matsayin ramuwar gayya kan hare-haren da bangarorin Falasdinawan da ke Lebanon suka kai mata, hakan ya sa aka samu kafuwar kungiyar Kuuma ta samu goyan bayan Iran, musamman ma daga dakarun da suka taimaka wajen juyin-juya halin kasar, inda suka taimaka musu da kudade, makamai da horo a kokarin fadada tasirin Iran a cikin kasashen Larabawa.
Kungiyar Sojojin Hizbullah ta ci gaba da samun ci gaba bayan kawo karshen yakin basasar Lebanon a shekarar 1990, duk kuwa da yadda akasarin kungiyoyin da suka taka rawa a yakin basasar sun suka kwance damara. Kungiyar ta ci gaba da mai da hankali kan ‘yantar da ‘ Labanon daga Isra’ila, kuma ta shafe shekaru da yawa tana yakin basasa da sojojin Isra’ila da suka mamaye Kudancin Lebanon har zuwa lokacin da Isra’ila ta fice a shekara ta 2000.

Labarai Masu Nasaba

Gwamna Yusuf Ya Kafa Kwamitin Bincikar Kwamishinan Sufuri Kan Karɓar Belin Dilan Ƙwaya A Kano

Dangote Ya Ajiye Muƙamin Shugabancin Kamfaninsa Na Siminti

Daga nan sai kungiyar Hizbullah ta mayar da hankali sosai wajen kwato yankin da ake takaddama a kan iyaka na gonakin Shebaa na Lebanon .

A shekarar 2006, Hizbullah ta shiga yakin makwanni biyar da Isra’ila a wani yunkuri na ‘yantar da Falasdinu. Rikicin da ya janyo asarar rayukan Isra’ilawa sama da 158 da kuma ‘yan Lebanon sama da 1,200, galibi fararen hula.

Daga shekarar 2011, lokacin yakin basasar Kasar Syria, karfi da tasirin kungiyar Hizbullah ya kara bayyana, saboda yadda dakarunta suka taimaka wa shugaban Syria Bashar al-Assad, wanda ke kawance da Iran, a kan galibin ‘yan tawayen da suke da akidar Sunni.

A shekarar 2021, shugaban Kungiyar Hizbullah, Hassan Nasrallah ya ce kungiyar na da mayaka 100,000.

Kungiyar Hizbullah na taka rawa a matsayin jam’iyyar siyasa a Lebanon. A shekara ta 1992 ne aka fara zaben wakilai takwas a majalisar dokokin kasar Lebanon. To sai dai kuma a shekarar 2018 kungiyar Hizbullah ta samu rinjaye a majalisar kasa inda ta kafa gwamnati.

Kungiyar Hizbullah ta ci gaba da rike kujeru 13 a zaben shekara ta 2022 amma kawancen ya rasa rinjayen da yake da shi kuma kasar a halin yanzu ba ta da cikakkiyar gwamnati mai aiki . Sauran jam’iyyun na Labanon na zargin kungiyar Hizbullah da gurgunta gwamnati da zagon kasa da kuma taimakawa wajen ci gaba da zaman lafiyar kasar Labanon.

Kungiyar Mayakan Hamas
Hamas, itama kalamar Larabci ce da ake fassara ta da “Kishi” wanda kuma kungiyar mayakan Hamas ke fassara ta “Juriya kan Musulunci”. An kafa kungiyar ne a shekarar 1987, a Gaza, a matsayin reshe na kungiyar ‘yan uwa Musulmi, karkashin jagorancin wata fitacciyar kungiyar Sunni da ke da cibiya a Masar.

A farkon lokaci, kungiyar Hamsa tana alla wadai ne da tofin ala tsine ga Isra’ilawa kan irin mamayar da suke musu da kuma yunkunrinsu na gallaza musu da kuma tauye musu hakkinsu.

Siyasar Falasdiwa ta sauya sosai bayan yarjejeniyar Oslo a shekarar 1993, da kuma wasu jerin yarjejeniyoyin da aka cimma tsakanin gwamnatin Isra’ila da kungiyar ‘yantar da Falasdinu (PLO) a matsayin cikkakkiyar yarjejeniyar zaman lafiya.
Saboda rashin gamsuwa da kuma adawa da waccar yarjejeniyar, wani bangare na Kungiyar Hamas masu dauke da makamai, na Al-Kassam Brigades, ya balle tare da tabbatar da kansu a matsayin babbar rundunar juriya da yaki da kasar Isra’ila.

Bangaren kungiyar ya fara kai hare-hare da kunar bakin wake (2000-2005), kafin kungiyar ta fara amfani da makaman roka.
Kamar Hizbullah, Hamas na ganin kanta a matsayin jam’iyyar siyasa, ta shiga tare da lashe zabbn ‘yan majalisar dokoki a shekarar 2006, da kuma shekarar 2007, ta sami iko da yankin Zirin Gaza a wani kazamin fada da jam’iyyar Fatah wanda suke gaba da juna, wanda ya yi sanadin mutuwar sama da mutane 100.

Hamas dai na rike da yankin Gaza tun daga lokacin, inda ta nuna rashin hakuri da ‘yan adawar siyasa. Ba su taba gudanar da zabe ba, kuma ana kama abokan hamayyar siyasa da masu suka.

A tsawon wannan lokaci, reshen Hamas da ke dauke da makamai ya kara samun kwarewa, tare da samun makamai, wanda suka hada da roka, bindigogi masu sarrafa kansu da dai sauaransu.

Yaya Hamas da Hizbullah suka bambanta?
Hamas dai na samun tallafin kudade da makamai da horarwa daga kasar Iran, amma ba a aljihun Iran din ba kamar yadda kungiyar Hizbullah ta ke samun goyon bayan Iran kadai, kuma tana karbar umarnin daga wajenta.

Sabanin haka, Hamas ta samu tallafi a baya daga Turkiyya da Katar, da dai sauransu, kuma tana gudanar da ayyukanta na cin gashin kai. Haka kuma kungiyar ta dade da rashin jituwa tsakaninta da Iran dangane da sabanin ra’ayinsu a Siriya.

A yanzu dai wannan yaki ne tsakanin Isra’ila da Hamas. Har yanzu dai Hezbollah na zama barazana ga Isra’ila. Idan Iran ta kunna ta, cikakken shigarta zai canza yanayin rikici cikin sauri kuma zai iya bude yakin yanki.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: FalasdinawaHamasHezbollahIsra'ila
ShareTweetSendShare
Previous Post

Me Ya Sa Kasar Sin Ke Son Ganin Nijeriya Ta Samu Ci Gaba Mai Inganci?

Next Post

Kiran Da Kasar Sin Ta Yi Na Samar Da Zaman Lafiya Tsakanin Isra’ila Da Falasdinu Wani Buri Ne Na Duniya Baki Daya

Related

Gwamnatin Kano Ta Gabatar Da Buƙatu 10 A Gaban Kwamitin Gyaran Tsarin Mulkin Nijeriya
Da ɗumi-ɗuminsa

Gwamna Yusuf Ya Kafa Kwamitin Bincikar Kwamishinan Sufuri Kan Karɓar Belin Dilan Ƙwaya A Kano

31 minutes ago
Dangote Ya Sake Zama Wanda Ya Fi Kowa Kudi A Afrika Karo Na 12
Manyan Labarai

Dangote Ya Ajiye Muƙamin Shugabancin Kamfaninsa Na Siminti

12 hours ago
Rayuwar Aso Rock: Shugabannin Nijeriya 4 Da Suka Mutu Bayan Kammala Wa’adin Mulki
Rahotonni

Rayuwar Aso Rock: Shugabannin Nijeriya 4 Da Suka Mutu Bayan Kammala Wa’adin Mulki

14 hours ago
Gwamnan Jigawa Ya Rattaba Hannu Kan Kudirin Dokar Tabbatar Da Hisbah
Labarai

Gwamnan Jigawa Ya Rattaba Hannu Kan Kudirin Dokar Tabbatar Da Hisbah

15 hours ago
Jihohin Da Ke Shirin Rage Kudin Wutar Lantarki Su Shirya Biyan Tallafi – Ministan Wuta
Labarai

Jihohin Da Ke Shirin Rage Kudin Wutar Lantarki Su Shirya Biyan Tallafi – Ministan Wuta

16 hours ago
majalisar kasa
Labarai

‘Yan Majalisa Sun Zargi Hukumomin Gwamnati Da Wawure Sama Da Naira Biliyan 103.8

17 hours ago
Next Post
Kiran Da Kasar Sin Ta Yi Na Samar Da Zaman Lafiya Tsakanin Isra’ila Da Falasdinu Wani Buri Ne Na Duniya Baki Daya

Kiran Da Kasar Sin Ta Yi Na Samar Da Zaman Lafiya Tsakanin Isra'ila Da Falasdinu Wani Buri Ne Na Duniya Baki Daya

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Kano Ta Gabatar Da Buƙatu 10 A Gaban Kwamitin Gyaran Tsarin Mulkin Nijeriya

Gwamna Yusuf Ya Kafa Kwamitin Bincikar Kwamishinan Sufuri Kan Karɓar Belin Dilan Ƙwaya A Kano

July 26, 2025
Manyan Nasarorin Da Dakta Dantsoho Ya Samar Tun Darewarsa Shugabancin NPA

Manyan Nasarorin Da Dakta Dantsoho Ya Samar Tun Darewarsa Shugabancin NPA

July 26, 2025
Gwamnatin Tarayya Na Shirin Dakatar Da Shigo Da Kifi Daga Ketare

Gwamnatin Tarayya Na Shirin Dakatar Da Shigo Da Kifi Daga Ketare

July 26, 2025
2027: Atiku, Obi Da Amaechi Za Su Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Takarar Shugaban Kasa A ADC

ADC Ga Tinubu: Ina Wutar Lantarki Ta Awa 24 Da Ka Yi Wa ‘Yan Nijeriya Alkawari?

July 26, 2025
Sin Da EU Suna Kokarin Samun Moriyar Juna A Shekaru 50 Masu Zuwa

Sin Da EU Suna Kokarin Samun Moriyar Juna A Shekaru 50 Masu Zuwa

July 25, 2025
Dalilin Da Ya Sa Har Yanzu Obi Da El-Rufai Ba Su Shiga ADC A Hukumance Ba — Kakakin Jam’iyyar 

Dalilin Da Ya Sa Har Yanzu Obi Da El-Rufai Ba Su Shiga ADC A Hukumance Ba — Kakakin Jam’iyyar 

July 25, 2025
Dangote Ya Sake Zama Wanda Ya Fi Kowa Kudi A Afrika Karo Na 12

Dangote Ya Ajiye Muƙamin Shugabancin Kamfaninsa Na Siminti

July 25, 2025
Binciken Jin Raayoyi Na CGTN: Duniya Ta Saba Da “Kauracewar” Amurka

Binciken Jin Raayoyi Na CGTN: Duniya Ta Saba Da “Kauracewar” Amurka

July 25, 2025
Jam’iyyar PDP Ta Janye Daga Shiga Zaɓen Ƙananan Hukumomi A Kebbi

2027: Masu Neman Takarar Shugaban Kasa A PDP Sun Kara Matsa Kaimi Bayan Ficewar Atiku

July 25, 2025
Xi Jinping Ya Karbi Takardun Nadi Daga Sabbin Jakadun Kasashen Waje

Xi Jinping Ya Karbi Takardun Nadi Daga Sabbin Jakadun Kasashen Waje

July 25, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.