ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, July 15, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kiran Da Kasar Sin Ta Yi Na Samar Da Zaman Lafiya Tsakanin Isra’ila Da Falasdinu Wani Buri Ne Na Duniya Baki Daya

by CGTN Hausa
3 years ago
Sin

Za a ci gaba da tashe-tashen hankula muddin ba a warware koke-koke da bambance-bambance dake tsakanin Falasdinawa da Isra’ila ba.

Rikicin da ake ciki a yanzu ya taso ne sakamakon watsi da ka’idojin Majalisar Dinkin Duniya da kuma yadda bangarorin biyu suka kasa daina kai hari kan fararen hula.

  • Matashin Dan Kwallon Barcelona Guiu Mai Shekaru 17 Ya Jefa Kwallon Farko A Kungiyar
  • “Hanyar Siliki Ta Dijital” Na Ingiza Zamanantar Da Duniya

La’akari da wannan matsalar ne Shugaban kasar Sin Xi Jinping, a yayin ganawarsa da firaministan Masar Mostafa Madbouly a nan birnin Beijing a ranar 19 ga watan Oktoba, ya bayyana cewa, “Muhimmiyar hanyar warware rikicin Palasdinu da Isra’ila da ke ci gaba da tabarbarewa, ita ce aiwatar da yarjejeniyar da aka cimma game da shirin kafa ‘kasashe biyu’, wato kafa kasar Falasdinu mai cin gashin kanta, ta yadda za a tabbatar da zaman lafiya tsakanin Falasdinu da Isra’ila.”

ADVERTISEMENT

 

Hanyar tabbatar da zaman lafiya ba hanya ce mai sauki ba, amma ana iya farawa da fahimtar bukatun dukkanin bangarorin dake cikin rikicin. Rikicin Isra’ila da Falasdinu ba shi ne tushen matsalar ba, sai dai ya samo asali ne daga wani yanki na babban yanayi na duniya wanda ke cike da zalunci da tsangwama, da halin mamaya da karfafa rarrabuwar kawuna. Wajibi ne a tunkari cibiyoyi da ra’ayoyin dake haifar da rarrabuwar kawuna da suka hada da na leken asiri bisa muradun kasashen yamma da wasu kafafen yada labarai masu rura wutar fitina, da kuma magance dukkan batutuwan da suke da nasaba da wanann rikicin da ba a san ranar karewarsa ba.

LABARAI MASU NASABA

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

 

Ya zama dole bangarorin da ke rikicin su yi la’akari da kiran da kasashen duniya suka yi na samar da “kasashe biyu” masu cin gashin kansu. Dole a fitar da Falasdinawa daga ukubar Isra’ila, kana, a bar su su mallaki kasarsu bisa tsare-tsare da ka’idoji da al’adun Falasdinawa kuma daidai da bukatunsu da dabi’unsu.

“Warware matsalar ta hanyar samar da kasashe biyu” na iya karfafa ci gaban tattalin arziki, saboda zai ba da ingantaccen tsarin tantance kan iyakoki, da inganta kasuwanci da tsaro ga Isra’ila da Falasdinawa. Kowace kasa za ta iya sanya nata matakan kasuwanci da tsaro da suka dace da al’ummarta da bukatunta idan an fayyace iyakokinta da kyau. Neman ci gaban tattalin arziki da inganta rayuwar Falasdinawa dake zaune a cikin kasa mai cin gashin kanta zai samar da zaman lafiya da wadata a yankin.

Babban abin takaicin shi ne, matsayin birnin Kudus a halin da ake ciki, da hakkin ’yan gudun hijirar Falasdinawa da aka dade ana ketawa, da kuma wuraren da Isra’ila take matsugunai a yammacin gabar kogin Jordan, na daga cikin manyan kalubale da cikas ga aiwatar da shirin na samar da “kasashen biyu”. Don warware wadannan matsalolin da samun ci gaba ga yarjejeniyar zaman lafiya mai dorewa, dole ne a yi nasara ta hanyar diflomasiyya da sasantawa.

Taimakon da kasar Sin take baiwa kokarin kasar Masar na kafa hanyoyin jin kai da kuma aniyyarta na inganta hadin gwiwa da kasar Masar da sauran kasashen Larabawa, wani mataki ne kan hanyar da ta dace ga jin kan Falasdinawa. Shugaba Xi ya bayyana cewa, kasar Sin a shirye take ta hada karfi da karfe tare da Masar da sauran kasashen Larabawa don inganta hadin gwiwar tattalin arziki a fannoni daban daban.

Zubar da jinin dake gudana ya zama gargadi mai ban tsoro na abin dake faruwa sa’ad da kuskure, da rarrabuwa kawuna, da rashin yarda suka ci gaba da wanzuwa. Abin takaici, bangarorin da abin ya shafa sun kasa ba da fifiko ga kariyar fararen hula, da rungumar akidar tabbatar daidaito da fahimta, da kuma sanin yadda gwagwarmayarsu ke da alaka da juna domin koyo daga kura-kurai. Ba abin mamaki ba ne suka kasa cimma manufar dawwamar da zaman lafiya ta hanyar ajiye bambance-bambancen da ke tsakaninsu.

Yin aiki tare, tsakanin Sin da kasashen Larabawa, musamman Masar, na iya ba da gudummawa ga irin wannan kuduri na lumana tsakanin Isra’ila da Falasdinu. Karfafa tsagaita bude wuta, kaddamar da kasuwanci da fadada tattalin arziki, da hadin gwiwar diflomasiyya, duk suna aiki tare don samar da yanayin da zai dace da tattaunawar zaman lafiya da kuma matakan da aka amince da su.

Sin
CGTN Hausa
+ postsBio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

MASU ALAKA

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya
Daga Birnin Sin

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

July 14, 2026
Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026
Daga Birnin Sin

Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

July 14, 2026
An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”
Daga Birnin Sin

An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

July 14, 2026
Next Post
Mun Damu Kan Bayyanar Mayakan Kungiyar Ansaru A Yankinmu — Mutanen Birnin Gwari

Mun Damu Kan Bayyanar Mayakan Kungiyar Ansaru A Yankinmu — Mutanen Birnin Gwari

LABARAI MASU NASABA

‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi

‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

‘Yansanda Sun Kama Wani Kan Zargin Yi Wa ‘Yan Bindiga Safarar Makamai A Kano

July 15, 2026
Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

July 14, 2026
Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

July 14, 2026
An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

July 14, 2026
Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

July 14, 2026
Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

July 14, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga

Kotu Ta Tsare Shugaban Makaranta Da Malami Kan Zargin Lalata Da Ɗaliba Mai Shekara 6 A Gombe

July 14, 2026
An Bankado Muguwar Aniyar Japan Ta Haifar Da Tashin Hankali A Tekun Kudancin Sin

An Bankado Muguwar Aniyar Japan Ta Haifar Da Tashin Hankali A Tekun Kudancin Sin

July 14, 2026
Layin Dogo Tsakanin Tanzaniya Da Zambiya Ya Zama Shaidar Abota Tsakanin Sin Da Afirka

Layin Dogo Tsakanin Tanzaniya Da Zambiya Ya Zama Shaidar Abota Tsakanin Sin Da Afirka

July 14, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.