• English
  • Business News
Wednesday, July 16, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kiran Da Kasar Sin Ta Yi Na Samar Da Zaman Lafiya Tsakanin Isra’ila Da Falasdinu Wani Buri Ne Na Duniya Baki Daya

by CGTN Hausa
2 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Kiran Da Kasar Sin Ta Yi Na Samar Da Zaman Lafiya Tsakanin Isra’ila Da Falasdinu Wani Buri Ne Na Duniya Baki Daya
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Za a ci gaba da tashe-tashen hankula muddin ba a warware koke-koke da bambance-bambance dake tsakanin Falasdinawa da Isra’ila ba.

Rikicin da ake ciki a yanzu ya taso ne sakamakon watsi da ka’idojin Majalisar Dinkin Duniya da kuma yadda bangarorin biyu suka kasa daina kai hari kan fararen hula.

  • Matashin Dan Kwallon Barcelona Guiu Mai Shekaru 17 Ya Jefa Kwallon Farko A Kungiyar
  • “Hanyar Siliki Ta Dijital” Na Ingiza Zamanantar Da Duniya

La’akari da wannan matsalar ne Shugaban kasar Sin Xi Jinping, a yayin ganawarsa da firaministan Masar Mostafa Madbouly a nan birnin Beijing a ranar 19 ga watan Oktoba, ya bayyana cewa, “Muhimmiyar hanyar warware rikicin Palasdinu da Isra’ila da ke ci gaba da tabarbarewa, ita ce aiwatar da yarjejeniyar da aka cimma game da shirin kafa ‘kasashe biyu’, wato kafa kasar Falasdinu mai cin gashin kanta, ta yadda za a tabbatar da zaman lafiya tsakanin Falasdinu da Isra’ila.”

 

Hanyar tabbatar da zaman lafiya ba hanya ce mai sauki ba, amma ana iya farawa da fahimtar bukatun dukkanin bangarorin dake cikin rikicin. Rikicin Isra’ila da Falasdinu ba shi ne tushen matsalar ba, sai dai ya samo asali ne daga wani yanki na babban yanayi na duniya wanda ke cike da zalunci da tsangwama, da halin mamaya da karfafa rarrabuwar kawuna. Wajibi ne a tunkari cibiyoyi da ra’ayoyin dake haifar da rarrabuwar kawuna da suka hada da na leken asiri bisa muradun kasashen yamma da wasu kafafen yada labarai masu rura wutar fitina, da kuma magance dukkan batutuwan da suke da nasaba da wanann rikicin da ba a san ranar karewarsa ba.

Labarai Masu Nasaba

Xi Jinping Ya Mika Sakon Ta’aziyya Zuwa Ga Takwaransa Na Najeriya Bisa Rasuwar Muhammadu Buhari

Sin Ta Yi Nasarar Harba Kumbon Dakon Kaya Na Tianzhou-9

 

Ya zama dole bangarorin da ke rikicin su yi la’akari da kiran da kasashen duniya suka yi na samar da “kasashe biyu” masu cin gashin kansu. Dole a fitar da Falasdinawa daga ukubar Isra’ila, kana, a bar su su mallaki kasarsu bisa tsare-tsare da ka’idoji da al’adun Falasdinawa kuma daidai da bukatunsu da dabi’unsu.

“Warware matsalar ta hanyar samar da kasashe biyu” na iya karfafa ci gaban tattalin arziki, saboda zai ba da ingantaccen tsarin tantance kan iyakoki, da inganta kasuwanci da tsaro ga Isra’ila da Falasdinawa. Kowace kasa za ta iya sanya nata matakan kasuwanci da tsaro da suka dace da al’ummarta da bukatunta idan an fayyace iyakokinta da kyau. Neman ci gaban tattalin arziki da inganta rayuwar Falasdinawa dake zaune a cikin kasa mai cin gashin kanta zai samar da zaman lafiya da wadata a yankin.

Babban abin takaicin shi ne, matsayin birnin Kudus a halin da ake ciki, da hakkin ’yan gudun hijirar Falasdinawa da aka dade ana ketawa, da kuma wuraren da Isra’ila take matsugunai a yammacin gabar kogin Jordan, na daga cikin manyan kalubale da cikas ga aiwatar da shirin na samar da “kasashen biyu”. Don warware wadannan matsalolin da samun ci gaba ga yarjejeniyar zaman lafiya mai dorewa, dole ne a yi nasara ta hanyar diflomasiyya da sasantawa.

Taimakon da kasar Sin take baiwa kokarin kasar Masar na kafa hanyoyin jin kai da kuma aniyyarta na inganta hadin gwiwa da kasar Masar da sauran kasashen Larabawa, wani mataki ne kan hanyar da ta dace ga jin kan Falasdinawa. Shugaba Xi ya bayyana cewa, kasar Sin a shirye take ta hada karfi da karfe tare da Masar da sauran kasashen Larabawa don inganta hadin gwiwar tattalin arziki a fannoni daban daban.

Zubar da jinin dake gudana ya zama gargadi mai ban tsoro na abin dake faruwa sa’ad da kuskure, da rarrabuwa kawuna, da rashin yarda suka ci gaba da wanzuwa. Abin takaici, bangarorin da abin ya shafa sun kasa ba da fifiko ga kariyar fararen hula, da rungumar akidar tabbatar daidaito da fahimta, da kuma sanin yadda gwagwarmayarsu ke da alaka da juna domin koyo daga kura-kurai. Ba abin mamaki ba ne suka kasa cimma manufar dawwamar da zaman lafiya ta hanyar ajiye bambance-bambancen da ke tsakaninsu.

Yin aiki tare, tsakanin Sin da kasashen Larabawa, musamman Masar, na iya ba da gudummawa ga irin wannan kuduri na lumana tsakanin Isra’ila da Falasdinu. Karfafa tsagaita bude wuta, kaddamar da kasuwanci da fadada tattalin arziki, da hadin gwiwar diflomasiyya, duk suna aiki tare don samar da yanayin da zai dace da tattaunawar zaman lafiya da kuma matakan da aka amince da su.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: FalasdinuSin
ShareTweetSendShare
Previous Post

Asalin Kungiyoyin Mayakan Hamas, Hizbullah Da Manufofinsu

Next Post

Mun Damu Kan Bayyanar Mayakan Kungiyar Ansaru A Yankinmu — Mutanen Birnin Gwari

Related

Xi Jinping Ya Mika Sakon Ta’aziyya Zuwa Ga Takwaransa Na Najeriya Bisa Rasuwar Muhammadu Buhari
Daga Birnin Sin

Xi Jinping Ya Mika Sakon Ta’aziyya Zuwa Ga Takwaransa Na Najeriya Bisa Rasuwar Muhammadu Buhari

23 minutes ago
Sin Ta Yi Nasarar Harba Kumbon Dakon Kaya Na Tianzhou-9
Daga Birnin Sin

Sin Ta Yi Nasarar Harba Kumbon Dakon Kaya Na Tianzhou-9

19 hours ago
Xi Ya Gana Da Shugabannin Tawagogin Kasa Da Kasa Masu Halartar Taron SCO
Daga Birnin Sin

Xi Ya Gana Da Shugabannin Tawagogin Kasa Da Kasa Masu Halartar Taron SCO

21 hours ago
An Gudanar Da Taro Game Da Sana’ar Sarrafa Sinadarai Na Kasa Da Kasa Karo Na 12 A Beijing
Daga Birnin Sin

An Gudanar Da Taro Game Da Sana’ar Sarrafa Sinadarai Na Kasa Da Kasa Karo Na 12 A Beijing

21 hours ago
Yawan Karuwar GDPn Sin A Rabin Farkon Bana Ya Kai 5.3%
Daga Birnin Sin

Yawan Karuwar GDPn Sin A Rabin Farkon Bana Ya Kai 5.3%

22 hours ago
Shugaba Xi Ya Gabatar Da Jawabi Ga Taron Koli Game Da Aikin Raya Birane 
Daga Birnin Sin

Shugaba Xi Ya Gabatar Da Jawabi Ga Taron Koli Game Da Aikin Raya Birane 

23 hours ago
Next Post
Mun Damu Kan Bayyanar Mayakan Kungiyar Ansaru A Yankinmu — Mutanen Birnin Gwari

Mun Damu Kan Bayyanar Mayakan Kungiyar Ansaru A Yankinmu — Mutanen Birnin Gwari

LABARAI MASU NASABA

Afrika Ta Zama Kasuwar Sayar Da Man Fetur Mara Inganci – Dangote

Afrika Ta Zama Kasuwar Sayar Da Man Fetur Mara Inganci – Dangote

July 16, 2025
Xi Jinping Ya Mika Sakon Ta’aziyya Zuwa Ga Takwaransa Na Najeriya Bisa Rasuwar Muhammadu Buhari

Xi Jinping Ya Mika Sakon Ta’aziyya Zuwa Ga Takwaransa Na Najeriya Bisa Rasuwar Muhammadu Buhari

July 16, 2025
An Fara Binciken Mutuwar Wasu Ɗalibai 2 A Makarantar Kwana A Kano

An Fara Binciken Mutuwar Wasu Ɗalibai 2 A Makarantar Kwana A Kano

July 16, 2025
Atiku Abubakar Ya Fice Daga PDP, Duba Dalili

Atiku Abubakar Ya Fice Daga PDP, Duba Dalili

July 16, 2025
Peter Obi Ya Kai Wa Iyalan Buhari Ziyarar Ta’aziyya

Peter Obi Ya Kai Wa Iyalan Buhari Ziyarar Ta’aziyya

July 16, 2025
Nijeriya Na Fuskantar Siyasa Mara Tabbas —  Peter Obi

Omokri Da Sarki Sun Soki Obi Saboda Rashin Halartar Jana’izar Buhari

July 16, 2025
Kotu Ta Wanke Fayose Daga Zargin Zambar Naira Biliyan 3.3

Kotu Ta Wanke Fayose Daga Zargin Zambar Naira Biliyan 3.3

July 16, 2025
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

July 16, 2025
An Fara Biyan Ma’aikata Sabon Mafi Ƙarancin Albashin N70,000 A Borno

Yara 2 Sun Kuɓuta Bayan Shafe Shekaru 6 A Hannun Boko Haram A Borno

July 16, 2025
Kasa Da Wata Biyu Ya Bar Mulki, Shin Ko Buhari Ya Cika Wa ‘Yan Nijeriya Alkawarin Da Ya Yi Mu Su?

EU, Turkiyya Da Sauran Ƙasashe Sun Yi Ta’aziyyar Rasuwar Buhari

July 16, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.