ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Monday, June 22, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Jihohin Da Ke Shirin Rage Kudin Wutar Lantarki Su Shirya Biyan Tallafi – Ministan Wuta

by Sani Anwar and Sulaiman
11 months ago
Lantarki

Gwamnatin tarayya ta dauki tsattsauran mataki game da jihohin da suka zabi rage kudin wutar lantarki, inda ta bayyana cewa; alhakin tallafin da ya dace a biya, ya zama dole ya koma kan jihohin.

Ma’aikatar wutar lantarki, wacce ta bayyana hakan ta bayyana cewa; ba ta da niyyar yi wa hukumomi masu cin gashin kansu katsalandan, amma kuma tana sa ran za su yi la’akari da yadda abubuwa ke kasancewa na zahiri kafin su kai ga yanke shawarar rage wannan kudin wuta.

  • Majalisa Ta Ba Wa Shugaban NNPCL Awa 24 Ya Bayyana Gabanta Ko Ta Sa A Kamo Shi
  • Tinubu Na Yi Wa Arewa Manyan Ayyuka – Martanin Fadar Shugaban Ƙasa Ga Kwankwaso 

Kamar yadda kwamishinan wutar lantarki da sabunta makamashi na Jihar Benuwai kuma shugaban kungiyar kwamishinonin wutar lantarki da makamashi a Nijeriya, Barista Omale Omale, ya kare matakin da hukumar kula da wutar lantarki ta Inugu (EERC), ta dauka na rage farashin wutar lantarki ga kwastomomin kamfanin Rukunin A (Band A) a jihar.

ADVERTISEMENT

Har ila yau, matakin ya haifar da martani da dama a cikin sashen samar da wutar lantarki a masana’antar, Omale ya ce; tsarin jadawalin biyan kudin wutar yanzu a Jihar Inugu, kamar yadda EERC ta kididdige, ya fi kama da abin da hankali zai dauka.

Hukumar kula da wutar lantarki ta Jihar Inugu ta sanar da cewa, babban kamfanin da ke kula da rarraba wutar lantarki, sabon kamfanin raba lasisi na Jihar Inugu, zai rage farashin Rukunin A (Band A), zuwa Nair 160 kam kowane kwh, maimakon Naira 209 da ake saya, inda kuma Rukunin B zuwa E; za su ci gaba da saya kamar yadda suka saba.

LABARAI MASU NASABA

Fisatattun Matasa Sun Ƙone Wata Mata Ƙurmus Kan Jita-Jitar Satar Yara A Kaduna

Mutane 842 Ne Suka Rasa Ransu, Aka Yi Garkuwa Da Sama Da 270 A Watan Mayu – Rahoto

Bayan wannan mataki kuma, jihohi bakwai da suke da ruwa da tsaki kan harkokin wutar lantarkinsu, karkashin dokar 2023; na fuskantar matsin lamba a kan su sake duba kudaden da ake biya na wutar lantakin, bayan hukumar EERC ta fitar da wani muhimmin mataki na rage farashin wutar lantarkin na sashen Rukunin A (Band A), da kashi 24 cikin 100; wato daga Naira 209 zuwa Naira 160, tun daga 1 ga watan Agustan 2025.

Da yake zantawa da LEADERSHIP, mai bai wa ministan wutar lantarki shawara na musamman kan dabarun sadarwa da kafafen yada labarai, Bolaji Tunji ya ce; idan jihohi suka zabi rage kudin wutar lantarki, ya zama wajibi su kasance cikin shiri, don samar da kudaden tallafin da ake samu sakamakon wannan ragi, maimakon kara wa gwamnatin tarayya nauyi da tallafin da a yanzu haka; yah aura sama da Naira tiriliyan biyan a fannin samar da wutar lantarkin.

Har ila yau, ya kuma jaddada cewa; yayin da jihohi ke da ‘yancin cin gashin kai, kan kayyade kudin wutar lantarki, cin gashin kan ya zo ne tare da yin la’akari da abubuwan da suka shafi kudi.

Lantarki
Sani Anwar
+ posts Bio
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Tattalin Arziƙin Ƙasa: Masana Sun Buƙaci Tinubu Ya Yi Hattara Da Shawarar IMF
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Cututtukan Da Aka Fi Fama Da Su Lokacin Damina Da Yadda Za A Kauce Musu (2)
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Cututtukan Da Aka Fi Fama Da Su Lokacin Damina Da Yadda Za A Kauce Musu (1)
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Talauci Ya Sake Karuwa Da Kashi 63 Duk Da Sauye-sauyen Tattalin Arzikin Da Gwamnati Ta Yi – IMF
Lantarki
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Cibiyar CBA Ta Kenya Za Ta Yi Hadin Gwiwa Da Wata Cibiyar Sin Wajen Bunkasa Noma Da Cinikayyar Lemar Kwadi
  • Sulaiman
    An Sanar Da Wadanda Suka Lashe Golden Goblet Na Bikin Fina-Finen Kasa Da Kasa Na Shanghai Karo Na 28
  • Sulaiman
    Nasiha Ga Uwargida Kan Zafin Kishi (1)
  • Sulaiman
    Kasar Sin Ta Karbi Bakuncin Taron Daidaita Batun Kare Hakkin Dan Adam

MASU ALAKA

Fisatattun Matasa Sun Ƙone Wata Mata Ƙurmus Kan Jita-Jitar Satar Yara A Kaduna
Labarai

Fisatattun Matasa Sun Ƙone Wata Mata Ƙurmus Kan Jita-Jitar Satar Yara A Kaduna

June 22, 2026
Labarai

Mutane 842 Ne Suka Rasa Ransu, Aka Yi Garkuwa Da Sama Da 270 A Watan Mayu – Rahoto

June 21, 2026
PRP Ta Zargi Kwankwaso Da Saye Fom Ɗin Takarar  Jamiyyar
Manyan Labarai

PRP Ta Zargi Kwankwaso Da Saye Fom Ɗin Takarar Jamiyyar

June 21, 2026
Next Post
Kamfanin Sinotruk Na Kasar Sin Ya Kaddamar Da Sabbin Motocin Dakon Kaya A Kenya

Kamfanin Sinotruk Na Kasar Sin Ya Kaddamar Da Sabbin Motocin Dakon Kaya A Kenya

LABARAI MASU NASABA

Fisatattun Matasa Sun Ƙone Wata Mata Ƙurmus Kan Jita-Jitar Satar Yara A Kaduna

Fisatattun Matasa Sun Ƙone Wata Mata Ƙurmus Kan Jita-Jitar Satar Yara A Kaduna

June 22, 2026

Mutane 842 Ne Suka Rasa Ransu, Aka Yi Garkuwa Da Sama Da 270 A Watan Mayu – Rahoto

June 21, 2026
PRP Ta Zargi Kwankwaso Da Saye Fom Ɗin Takarar  Jamiyyar

PRP Ta Zargi Kwankwaso Da Saye Fom Ɗin Takarar Jamiyyar

June 21, 2026
An Ƙaddamar Da Dakarun Tsaron Daji 2,187 A Bauchi

An Ƙaddamar Da Dakarun Tsaron Daji 2,187 A Bauchi

June 21, 2026
An Sanar Da Wadanda Suka Lashe Golden Goblet Na Bikin Fina-Finen Kasa Da Kasa Na Shanghai Karo Na 28

An Sanar Da Wadanda Suka Lashe Golden Goblet Na Bikin Fina-Finen Kasa Da Kasa Na Shanghai Karo Na 28

June 21, 2026
Cibiyar CBA Ta Kenya Za Ta Yi Hadin Gwiwa Da Wata Cibiyar Sin Wajen Bunkasa Noma Da Cinikayyar Lemar Kwadi

Cibiyar CBA Ta Kenya Za Ta Yi Hadin Gwiwa Da Wata Cibiyar Sin Wajen Bunkasa Noma Da Cinikayyar Lemar Kwadi

June 21, 2026
Wasu Abubuwa Da Ke Sa Maza Hana Mata Fita Unguwa (Uwargida)

Nasiha Ga Uwargida Kan Zafin Kishi (1)

June 21, 2026
Kasar Sin Ta Karbi Bakuncin Taron Daidaita Batun Kare Hakkin Dan Adam

Kasar Sin Ta Karbi Bakuncin Taron Daidaita Batun Kare Hakkin Dan Adam

June 21, 2026
Wakilin Sin Ya Yi Jawabi A Taron Majalissar UNHRC

Wakilin Sin Ya Yi Jawabi A Taron Majalissar UNHRC

June 21, 2026
Ƴan Ta’adda Sun Ƙone Shingen Bincike Na NSCDC, Sun Sace Wani Mutum A Kebbi

Ƴan Ta’adda Sun Ƙone Shingen Bincike Na NSCDC, Sun Sace Wani Mutum A Kebbi

June 21, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.