Ranar 12 ga watan Yuli, rana ce ta cika shekaru 10 da fitar da takardar “hukuncin tekun kudancin Sin” da aka yanke wa kasar Sin ba bisa ka’ida ba. Kamar yadda ake tsammani, Philippines da wasu kasashen yamma sun hada baki, tare da sake yin amfani da wannan takarda marar amfani don tayar da zaune tsaye.
Tun daga tsakiyar watan Yuni, manyan kafafen yada labarai na Philippines suka kara wa miya gishiri game da hukuncin, inda wasu ‘yan siyasa kamar ministan tsaron Philippines suka zargi Sin da rashin karba da kuma rashin amincewa da hukuncin.
Kasashen Amurka, da Japan, da Birtaniya, da Austriliya, da Kanada da sauransu sun fitar da abin da ake kira “Sanarwa ta hadin gwiwa”, inda suka yi zargin cewa, ikon da Sin ta dade tana yi a tarihi a yankin tekun kudancinta ba shi da wata hujja bisa doka.
Amma kuma, duk yadda suka dauki matakai na rashin imani, ba za su canza gaskiyar lamari ba wato hukuncin ba shi da tushe balle makama, kana marar amfani ne, kuma ba shi da karfin hujja. Wannan hukunci na rashin imani, ba zai yi tasiri ko kadan kan ikon mallaka na kasar Sin a kan tsibiran tekun kudancinta, da sauran hakkokin teku ta kowace fuska ba.Abin da ya kamata a kula da shi shi ne, tun lokacin da aka fitar da hukuncin shekaru goma da suka gabata, har zuwa yadda Philippines ke ci gaba da tsokanar Sin a tekun kudancin Sin tsawon shekaru goma, ba shakka kasashen waje su kan kara wa miya gishiri.
Masanin cibiyar binciken tekun kudancin Sin ta kasar Sin, Chen Xiangmiao, ya nuna cewa, wasu kasashe kamar Amurka da kasashen yamma suna zuga Philippines da ta yi adawa da Sin a kan batun tekun kudancin Sin, kuma suna ta yayata batun hukuncin, don tada zaune tsaye a tekun kudancin Sin da nufin kuntata wa kasar Sin, kuma su yi amfani da hakan wajen zargin Sin da “lalata” dokokin kasa da kasa, da kuma bata sunan Sin a duniya.
A halin yanzu, yanayin tekun kudancin Sin yana cikin kwanciyar hankali bisa kokarin da Sin da yawancin kasashen ASEAN suka yi. Idan Philippines ta ci gaba da yin amfani da wannan hukunci maras amfani wanda aka yanke ba bisa doka ba, har ma da tsokanar Sin bisa hakan, da kuma kawo cikas ga zaman lafiya a yankin, to lallai za ta girbi abin da ta shuka. (Amina Xu)













