A safiyar yau 13 ga watan, an bude taron tattaunawa kan tsaron tekun kudancin Sin a birnin Hong Kong. A yayin taron, an fitar da rahoton “Sake karyata hukuncin tekun kudancin Sin”, hukuncin da Philippines ta jingina wa kasar Sin ba bisa doka ba. Wakilan fannin shari’a da masana da kwararru daga kasashe da yankuna daban-daban sun halarci taron.
Rahoton “Sake karyata hukuncin tekun kudancin Sin” wani nazari da kimantawa ne kan tasirin wannan hukunci da Philippine ta dora kan kasar Sin a shekara ta 2016, wato bayan shekaru goma da aka yanke shi.
An kuma sake yin nazari mai zurfi kan wannan hukunci daga mahangar masana.Rahoton ya nuna cewa, a cikin shekaru goma da suka gabata, wannan hukunci ba shi da tasiri sosai a kan irin wannan ayyukan shari’a da aka gudanar a kasa da kasa, kuma bangarorin masana na daukar matsayin adawa da wannan hukunci, saboda ya kasance maras tushe a bisa tsarin doka.(Amina Xu)














