Kamfanin dillancin labarai na Xinhua ya tattauna da mataimakin gwamnan bankin raya nahiyar Afrika (AFDB) Kevin Chika Urama, inda ya ce nan gaba kadan Afrika na da damar taka muhimiyyar rawa a tsarin tattalin arzikin duniya, bisa wasu fa’idoji kamar na yawan jama’a da albarkatu da nahiyar ke da su.
Amma me ya sa mataimakin gwamnan AFDB ke da wannan fata? Nahiyar Afrika ta shafe tsawon lokaci karkashin turawan mulkin mallaka, wanda har yanzu kasashe da dama na nahiyar ba su daina fama da mummunan tasirin hakan ba. Amma tasowar kasar Sin da ci gaban da take samu da yadda ta tsaya kai da fata wajen kare muradun kasashe masu tasowa, ya bude wa kasashen Afrika ido da ma kofa da fatan cewa, su ma za su iya tsayawa da kafarsu, kuma suna da abubuwan da suka cancanta na samun ci gaba. A cewar Kevin Chika Urana, tsarin na tattalin arzikin duniya na karkata ga cudanyar bangarori da dama maimakon wasu ’yan tsiraru. Godiya ga kasar Sin saboda ita ce ta jajirce wajen ganin an yi wa tsarin duniya garambawul, karkashin shawarwarin da ta gabatar kamar ta inganta shugabancin duniya wadda ke da nufin ganin dukkan kasashe sun hadu sun bayar da gudunmuwa da kara wakilcin kasashe masu tasowa ta yadda za a rika jin muryoyinsu da yin la’akari da ra’ayoyinsu, sabanin yadda ake aiwatar da manufofi ba tare da tuntubarsu.
Ci gaban kasar Sin wani kwarin gwiwa ya samar wa kasashe masu tasowa musamman na Afrika. Domin ta nuna musu cewa, za su iya tsara hanyar da ta dace da yanayi da al’ummominsu, kuma su samu ci gaban da suke fata. Yadda take kara hada gwiwa da tallafa musu ba tare da sharadi ko katsalandan ba, shi ma ya gabatar musu da wata sabuwar dabara ta hadin gwiwa ba tare da sun yi watsi da akidu da al’adunsu ba.
Idan muka duba fannin kasuwanci, musamman yadda Sin ta ba kasashen Afrika masu huldar diplomaisyya da ita damar shigo da kayayyaki kasar ba tare da biyan haraji ba, daya ne daga cikin hanyoyin taimakawa bunkasa karfin kasashen a bangarori da dama na tattalin arziki, domin ya kara musu kuzarin sarrafa albarkatu a cikin gida da samar da guraben ayyukan yi da habaka fitar kayayyakinsu da kara shiga kasuwannin duniya da karfin takara.
Wadannan kalilan ne daga cikin gudunmawar da Sin ke ba kasashen Afrika, shi ya sa har kullum nake cewa, ci gaban kasar Sin, ci gaba ne ga kasashen Afrika kuma dama ce ga daukacin kasashen duniya. (Faeza Mustapha)














