• English
  • Business News
Wednesday, October 15, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Abubuwan Da Ake Sa Ran Kwamitin Binciken Kananan Asibitoci Zai Gano

by Idris Aliyu Daudawa
3 years ago
Ran

Hukumar bunkasa kiwon lafiya matakin farko ta kasa ta kaddamar ta kwamiti mai zaman kansa, da zai gano matsalolin da suke damuwar asibitoci a fadin Nijeriya.

Babban jami’i kuma shugaban hukumar NPHCDA, Dakta Faisal Shuaib shi ne ya kaddamar da kwamitin a Abuja Babban Birnin Tarayya, ya bayyana cewa gwamnatocin tarayya, Jihohi, da kananan hukumomi sun sa kudade masu yawa a tsarin tafiyar da kula da lafiyar al’umma matakin farko.

  • Nnamdi Kanu Ya Maka Gwamnatin Tarayya A Kotun Koli 
  • Tinubu Ya Bukaci Manyan Masu Kalubalantarsa Atiku Da Obi Da Su Janye Daga Takara

Sai dai kuma duk da kudaden da suka sa har yanzu basu ga wani cigaban azo a gani ba, tunda har yanzu ana samun mutuwar mata masu juna biyu da kananan yara.

Yace “A shekaru biyu da suka gabata an samu cigaba mai gamsarwa, amma shi ma din bai kai ace an yaba ba, bai kuma dace da abinda ya dace mu samu a matsayinmu na kasa.Wannan shi yasa mu yin aiki tare da gidauniyar Dangote da ta Bill da Gate ga kuma ta Gwamnonin.Ga asusun kula da al’amuran gaggawa na kananan yara na majalisar dinkin duniya, Hukumar lafiya ta duniya,Taraiyar Turai, Bankin duniya,ga kungiyar cigaban kasa da kasa ta kasar Amurka.Hakan shi yasa muke ganin zuwa yanzun muna iya yin magana kan cigaban da aka samu, kan wani alkawarin da aka dauka na Seattle domin mun ga irin gudunmawar da Jihohi suka bada dangane da su kananan Asibitoci”.

Faisal yace wannan shi ne dalilin da yasa suka kasance cikin murna da jin dadi a Hukumar ta kula da lafiya matakin farko ta kasa, ma’aikatar lafiya ta Tarayya da sauran ‘yan kwamitin kulawa suna da mashahuran ‘yan Nijeriya daga Malaman manyan makarantu kan taimakon da suke yi ma al’umma.Ya kara jaddada cewa hukumar tana jiran tayi aiki da kwamitin domin kara bunkasa ayyukan wuraren kula da lafiyar al’umma matakin farko.

LABARAI MASU NASABA

Masana Sun Bayyana Yadda Za A Magance Ficewar Kamfanoni Da Masana’antu Daga Nijeriya

Ranar Malamai Ta Duniya: Rashin Kulawa Ke Sa Malamai Barin Aiki

Da take jawabi lokacin kaddamarwa jami’a, mai wakiltar ofishin asusun kula da al’amuran gaggawa na kananan yara na majalisar dinkin duniya na Nijeriya, Cristian Munduate ta nuna jin dadinta a kasance cikin wadanda za ayi abinda zai zama tarihi, na kokarin da ake na kara inganta kulawa da lafiyar al’umma,a karkashin Kudurin da aka cimmawa  a zaman taron na Seatle.

Ta ce taron ya cimma dukkan sharuddan da suka kamata shi yasa ma kwamitin da zai lura da bada shawara kai tsaye da yin bayani kan kokarin da kowacce Jiha tayi, domin tabbatar da shi tsarin da aka yi kudurin amfani da shi, ya kasance akwai adalci, rikon amana, da kasancewa ko wanne lokaci aka bukaci sanin halin da ake ciki babu wani bata lokaci za a sani.

“Ta kara jan hankali wajen bayyana yadda hukuma UNICEF ta jajirce da ganin sai an aiwatar da duk matakan da aka dauka lokacin da aka yi taro a Legas dangane da matsalolin da ake fuskanta.Yana da kyau a tuna dacewa dukkan gwamnonin Jihohi 36 sun samu halartar taron da kansu, domin nuna a shirye suke su bada duk gudun mawar da ake son su bada don a cimma burin abinda aka sa gaba”.

Bugu da kari tace UNICEF a shirye take ta hada kai da Nijeriya da duk sauran wadanda ake tafiya tare domin tabbatarwa ‘yan Nijeriya suna samun dukkan abubuwan da suke bukata, na kula da lafiyarsu kamar yadda ya kamata, ba tare da shan wahalar yadda za a samu abin yin amfani wajen neman kula da lafiyar.

Shi ma Babban darekta na kungiyar gwamnoni ta Nijeriya Mista Asishana Okauru cewa yayi kungiyar  bata siyasa  bace, amma tana yin taro aklai- akai domin tattauna al’amuran da   tsare- tsaren da suka shafi abubuwan  kawo cigaban al’umma.

Yace shi kwamitin mai zaman kan da aka kaddamar zai iya gano Jihohi da gwamnonin wadanda suka kasa cimma abubuwan da aka amince da ayi hakan, ya gode masu mabobin kwamitin mai zaman kansa wajen amincewar da suka yi na aiki tare da kungiyar gwamnaoni ta Nijeriya.

“Hakanan ma  a shekarar 2016 Shugabannin kungiyar an karbi bakuncinsu a Ciato wanda gidauniyarby the Bill-gate da Dangote ,wanda daga karshe aka samu  wata matsaya da ake kira da suna  yarjewar Ciato. Babban abinda suka sa gaba shi ne hanyar da za ayi amfani da ita domin tabbatar da duk kudurorin an samu cim masu kamar dai yadda ya bayyana”.

Akauru yace akwai wata tawaga ta wasu kwararru mai zaman kanta wadda zata rika taimakawa wajen tabbatar da duk abubuwan da aka amince za ayi ana aiwatar dasu, sai dai manufa ita ce ana son su yi aikinsu na kwararru ba su sa kansu cikin siyasa ba, shi yasa ma suka hada kungiyoyin biyu domin aiki tare.

A nata jawabin shugabar kungiyar mai zaman kanta da zata rika sa ido kan yadda ake aiwatar da tsare- tsaren Farfesa Florence Ejembi cewa tayi babbar rana ce,domin tun lokacin Ministan lafiya Farfesa Ransom Kuti tun, a shekarar 1986,inda aka fara daukar matakai na kawo gyara a harkar kula da lafiya, wani  mataki nha kula da lafiyar al’umma bai daya bangaren mataki na farko.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Masana Sun Bayyana Yadda Za A Magance Ficewar Kamfanoni Da Masana’antu Daga Nijeriya
Rahotonni

Masana Sun Bayyana Yadda Za A Magance Ficewar Kamfanoni Da Masana’antu Daga Nijeriya

October 11, 2025
Ranar Malamai Ta Duniya: Rashin Kulawa Ke Sa Malamai Barin Aiki
Rahotonni

Ranar Malamai Ta Duniya: Rashin Kulawa Ke Sa Malamai Barin Aiki

October 11, 2025
Jami’ar Nsukka Ta Ce Shaidar Digirin Ministan Fasaha, Uche Nnaji, Ta Bogi Ce
Manyan Labarai

Jami’ar Nsukka Ta Ce Shaidar Digirin Ministan Fasaha, Uche Nnaji, Ta Bogi Ce

October 4, 2025
Next Post
Ra’ayoyinku A Kan Batun Hako Man Fetur A Yankin Bauchi Da Gombe

Ra’ayoyinku A Kan Batun Hako Man Fetur A Yankin Bauchi Da Gombe

LABARAI MASU NASABA

Tinubu Ya Nemi Jihohi Su Dakatar Da Karbar Haraji A Kan Masu Safarar Kayan Abinci

Haƙar Ma’adinai Ba Bisa Ƙa’ida Ba Barazana Ce Ga Tsaro A Yammacin Afirka – Tinubu

October 15, 2025
Gabar ‘Yan Bindiga A Tsakaninsu Ta Kara Tsanani A Zamfara

‘Yan Bindiga Sun Hana Manoma Girbi A Zamfara, Al’umma Na Neman Taimako

October 15, 2025
‘Yansanda Sun Ceto Mutum 21 Da Aka Sace, Sun Kwato N4.8m Kuɗin Fansa

‘Yansanda Sun Kama Mutum 105, Sun Ƙwato Ƙwayoyi Sama Da 5,000 A Jigawa

October 15, 2025
Sojoji Sun Kama Ƙasurgumin Ɗan Bindiga, Sun Kashe Shugaban IPOB

Sojoji Sun Ceto Mutum 9 Da Aka Sace A Kwara

October 15, 2025
Dalilin Da Ya Sa Mutane Ke Dawowa Jam’iyyar APC — Shettima

Dalilin Da Ya Sa Mutane Ke Dawowa Jam’iyyar APC — Shettima

October 15, 2025
Ma’aikatar Kasuwancin Sin Ta Yi Kira Ga Amurka Da Ta Shiga Tattaunawar Cinikayya Da Sahihiyar Zuciya

Ma’aikatar Kasuwancin Sin Ta Yi Kira Ga Amurka Da Ta Shiga Tattaunawar Cinikayya Da Sahihiyar Zuciya

October 14, 2025
Uwar Gidan Shugaban Sin Ta Ziyarci Wajen Nune-nunen Karfafawa Mata Gwiwa A Bangaren Fasahohin Zamani

Uwar Gidan Shugaban Sin Ta Ziyarci Wajen Nune-nunen Karfafawa Mata Gwiwa A Bangaren Fasahohin Zamani

October 14, 2025
Gidauniyar Sheikh Dahiru Bauchi Ta Tura Ɗalibai 117 Karatu Ƙasar Algeria 

Gidauniyar Sheikh Dahiru Bauchi Ta Tura Ɗalibai 117 Karatu Ƙasar Algeria 

October 14, 2025
Sin Tana Adawa Da Matakan Kuntatawa Na Amurka Kan Bangarorin Kasar Da Suka Shafi Harkokin Teku Da Jigila Da Ginin Jiragen Ruwa 

Sin Tana Adawa Da Matakan Kuntatawa Na Amurka Kan Bangarorin Kasar Da Suka Shafi Harkokin Teku Da Jigila Da Ginin Jiragen Ruwa 

October 14, 2025
Kotu

Kotu A Kano Ta Tsare Wani Mai Gidan Marayu Bisa Zargin Satar Yara Da Safararsu Zuwa Delta

October 14, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.