Shekaru 10 bayan zaman sulhu kan batun tekun kudancin Sin ya yanke hukunci, Japan wadda ba ta da ruwa da tsaki cikin batun, ta sake fara yin kalamai na takala. Ministan harkokin wajen Japan Toshimitsu Motegi ya fito fili yana kare hukuncin wanda ba ya bisa doron doka, yana sukar halaltattun muradun Sin. Wannan shiryayyen yunkuri na siyasa, ya bankado muguwar aniyar Japan ta tsoma baki cikin batun tekun kudancin Sin da kawo hargitsi a yankin.
Shekaru 10 da suka wuce, Japan ta buya, inda ta yi ta kirkiro hujjojin gabatar wa zaman sulhu, kuma yanzu bayan shekaru 10, ta fito fili tana ingiza Phillipines domin ta haifar da rikici a tekun kudancin Sin. Wannan ya nuna wa duniya a bayyane cewa, Japan daya ce daga cikin kasashen waje da ke haifar da tsaiko ga zaman lafiya da kwanciyar hankali a tekun kudancin Sin, kuma ayyukanta na kalubalantar tsarin duniya da dokokin duniya bayan yakin duniya na II, har ma da take muradu da burikan kasashen yankin.
Cikakken ikon Sin da hakkokinta a tekun kudancin kasar, na da dadadden tarihi kuma suna bisa doron doka, don haka hukuncin wanda ya sabawa doka, ba zai taba yin tasirin kansu ba.Duk wani yunkuri na kawo tsaiko a tekun kudancin Sin ba zai yi nasara ba. (Mai fassara: Mustapha Fa”iza)













