Tsohon Sanatan da ya wakilci Mazabar Sanatan Gombe ta Arewa kuma tsohon Mataimakin Kakakin Majalisar Wakilai, Usman Bayero Nafada, ya fice daga jam’iyyar PDP, inda ya danganta matakin da rikice-rikicen cikin gida da matsalolin shugabanci da suka addabi jam’iyyar.
Nafada, wanda kuma ya taɓa zama ɗan takarar gwamna na PDP a Jihar Gombe, ya bayyana hakan ne cikin wata wasiƙa mai ɗauke da kwanan watan 12 ga Yulin 2026, wadda ya aika wa Shugaban PDP na Mazaɓar Nafada ta Gabas da ke Ƙaramar Hukumar Nafada a Jihar Gombe.
Rahotanni sun nuna cewa shugaban jam’iyyar na mazabar ya karɓi wasiƙar a ranar 13 ga Yulin 2026.Duk da ficewarsa daga jam’iyyar, Nafada ya gode wa PDP bisa damar da ta ba shi wajen gina rayuwarsa ta siyasa a cikin sama da shekaru ashirin da suka gabata.
Ficewarsa ɗin ta zo ne kwana ɗaya kacal bayan Shugaban Jam’iyyar APC na ƙasa, Nentawe Yilwatda, ya kai masa ziyarar ban girma a gidansa tare da Gwamnan Jihar Gombe, Muhammadu Inuwa Yahaya, da ɗan takarar gwamnan APC na shekarar 2027, Jamil Isyaku Gwamna, da kuma Yunusa Yakubu.
Sai dai har yanzu Nafada bai bayyana jam’iyyar da zai koma ba, ko kuma ya sanar a hukumance cewa zai shiga wata jam’iyya, duk da alamun da ke nuna cewa yana iya komawa jam’iyyar APC mai mulki.













