Tsohon Ministan Yaɗa Labarai, Lai Mohammed, ya bayyana yadda tsohon Shugaban Nijeriya, marigayi Muhammadu Buhari, ya taɓa tambayarsa mutane nawa ya kashe saboda yawan yin azumi da yake yi.
Mohammed, ya ce lamarin ya faru ne lokacin da ya kai ziyara wajen Buhari a Kaduna tare da Shugaba Bola Tinubu da jigon jam’iyyar APC, Bisi Akande.
Ya bayyana cewa a lokutan ganawarsu, yakan ƙi cin abinci saboda yana yin azumi a ranakun Litinin da Alhamis.
Daga baya Buhari ya tambayi Tinubu dalilin da ya sa Lai ba ya yarda ya ci abinci a gidansa.
Mohammed, ya ce daga baya Buhari ya kira shi, cikin raha ya tambaye shi dalilin da ya sa yake yawan yin azumi, har ma ya tambaye shi ko ya taɓa kashe wani mutum ne.
Ya ce ya amsa wa Buhari cewa bai taɓa kashe kowa ba, sannan ya bayyana cewa yin azumi wani ɓangare ne na ibadarsa.
Mohammed, ya ce alaƙarsa da Buhari ta musamman ce, inda ya ce sun ci gaba da yin rayuwa tare da Buhari, bayan ya bar mulki.
Ya ƙara da cewa babbar dama ce a gare shi ya san Buhari kuma ya yi aiki tare da shi.













