Hukumar Yaƙi da Sha da Fataucin Miyagun Ƙwayoyi ta Ƙasa (NDLEA), ta bayyana shirinta na sanya hannu kan Yarjejeniyar Fahimtar Juna (MoU) da takwararta ta ƙasar Masar domin ƙarfafa haɗin gwiwa wajen yaƙi da shaye-shaye da fataucin miyagun ƙwayoyi.
Hukumar ta ce yarjejeniyar za ta mayar da hankali kan musayar bayanan sirri, gudanar da ayyukan haɗin gwiwa da horas da jami’ai, domin ƙarfafa dangantakar da ke tsakanin Nijeriya da Masar tare da yaƙi da ƙungiyoyin fataucin miyagun ƙwayoyi da ke aiki a faɗin nahiyar Afirka.
Shugaban kuma Babban Daraktan Hukumar NDLEA, Mohamed Buba Marwa, ne ya bayyana hakan lokacin da Jakadan ƙasar Masar a Nijeriya, Mohammed Fouad, ya kai masa ziyarar ban girma a hedikwatar hukumar da ke Abuja a ranar Talata.
A cikin wata sanarwa da Daraktan Yaɗa Labarai da Wayar da Kai na NDLEA, Femi Babafemi, ya fitar, Marwa ya jaddada muhimmancin ƙara ƙarfafa haɗin gwiwa tsakanin ƙasashen biyu domin tunkarar barazanar miyagun ƙwayoyi da ke ƙara ƙamari a duniya.














