Jam’iyyar ADC ta nemi a kama tare da gurfanar da Nafiu Bala Gombe, bayan Hukumar Zaɓe Mai Zaman Kanta ta Ƙasa (INEC) ta ƙaryata Iƙirarinsa na cewa ya samu damar shiga shafin tantance sunayen ‘yan takarar zaɓen 2027.
ADC ta ce bayanin da INEC ta fitar na cewa takardar da Bala ya fitar ta bogi ce.
Mai magana da yawun jam’iyyar na ƙasa, Mallam Bolaji Abdullahi, ya buƙaci INEC ta miƙa lamarin ga hukumomin tsaro domin gudanar da bincike da yiwuwar gurfanar da shi a gaban kotu.
Jam’iyyar ta zargi Bala da yin iƙirarin ƙarya da kuma ƙoƙarin lalata amincewar jama’a ga tsarin zaɓen Nijeriya.
Ta ce yin iƙirarin samun damar shiga shafin INEC da aka taƙaita wa wasu mutane babban ƙalubale ne ga martabar hukumar.
ADC ta yi gargaɗin cewa rashin ɗaukar mataki kan lamarin na iya bai wa wasu mutane dsr riƙa yaɗa bayanan ƙarya, haifar da ruɗani da kuma rage amincewar jama’a ga tsarin zaɓe.
Jam’iyyar ta ce batun ba wai na ADC kaɗai ba ne, har ma ya shafi kare martabar hukumomin gwamnati da tabbatar da cewa duk wanda ya yi iƙirarin ƙarya kan hukumomin ƙasa ya fuskanci hukunci bisa doka.













