Sojoji sun daƙile yunƙurin kai hari da wasu da ake zargi mayaƙan ISWAP suka yi a garin Cross Kauwa da ke ƙaramar hukumar Kukawa a Jihar Borno.
Rundunar Sojin Nijeriya ta ce ’yan ta’addan sun kai hari kan wani sansanin soji a daren ranar Asabar, amma sojojin sun musu ruwan wuta lamarin da ya tilasta musu ja da baya.
Jami’in Yaɗa Labarai na Operation HADIN KAI, Kyaftin Mohammed Goni, ya ce ’yan ta’addan sun yi ƙoƙarin kutsa wa sansanin sojin ne da misalin ƙarfe 10:20 na dare.
Ya ce amma sojojin sun gano su tare da daƙile harin.
Rundunar ta ce bayanan sirri sun nuna cewa ’yan ta’addan suna ƙoƙarin sace magungunan cutar kwalara daga yankin.
Ta ƙara da cewa cutar Kwalara ta ɓarke a sansanonin ISWAP.
A yayin wani aikin share fage bayan harin, sojoji sun gano wata kyamarar ɗaukar bidiyo da ake zargin mallakar wani mai ɗaukar hoton ISWAP ne da aka kashe a lokacin arangamar.
Sojojin sun ce kyamarar tana ɗauke da wasu hotunan ayyukansu da kuma abubuwan shirye-shiryensu.
Haka kuma, sojojin sun ƙwato alburusai, kakin sojoji da wasu kayayyakin yaƙi da mayaƙan suka bari yayin da suke tserewa.
Rundunar ta ce sojoji biyu sun samu raunuka a yayin musayar wuta, amma suna cikin ƙoshin lafiya bayan samun kulawa.
Rundunar Operation HADIN KAI ta ce wannan samame wani babban koma baya ne ga ISWAP, tare da tabbatar da cewa za ta ci gaba da ƙoƙarin kare al’umma da yaƙi da ayyukan ta’addanci a yankin Arewa maso Gabas.













