A yau ake cika shekaru 50 da bude layin dogo da ya hada Tanzaniya da Zambiya a hukumance. Game da hakan, kakakin ma’aikatar harkokin wajen Sin, Lin Jian, ya bayyana cewa layin dogon shaida ce ta abota tsakanin Sin da Afirka.
Ya ce Sin tana son yin aiki tare da Tanzaniya da Zambiya don gina wata hanya mai ’yancin kai da ci gaba da abota da farin ciki da kiyaye muhalli, da kuma zaman jituwa, ta yadda za su ba da gudummawa ga bunkasa zamanantar da kasashen uku da sauran kasashen yankin.
Lin Jian ya bayyana hakan ne a gun taron manema labarai na yau da kullum da aka gudanar yau Talata.
Bugu da kari, Lin ya bayyana cewa, Sin ta dade tana adawa da kuma yaki da ayyukan satar bayanai ta kwamfuta. Ya ce Sin tana ba da shawara ga wasu kasashen da abin ya shafa da kada su bari a yi amfani da su, kuma kada su zama masu taimaka wa gwamnatin Amurka wajen yada labarai maras gaskiya da ake kira da wai “hare-haren yanar gizo na Sin”.
Lin ya kuma jaddada cewa, hukuncin takkadamar “Philippines da China”, a zahiri wasa ce ta siyasa da aka boye a karkashin “doka”, kuma ba za ta yi tasiri ga manufofi da matsayin Sin na warware takaddamar ta hanyar tattaunawa da shawarwari tare da kasashen da abin ya shafa kai tsaye ba. Ban da haka kuma, ya yi kira ga bangaren Turai da ya yi taka tsantsan kan kalamai da ayyukansa, sannan ya daina goyon bayan “hukuncin” wanda ba ya bisa doka.
Dangane da halin da ake ciki a yankin Gabas ta Tsakiya, Lin ya ce Sin ta damu sosai game da sake barkewar rikicin soja a yankin Gulf, kuma tana kira ga dukkan bangarorin da abin ya shafa da su bi kiran da kasa da kasa da ma yankuna suka yi na samun zaman lafiya da kwanciyar hankali, sannan su yi biyayya ga yarjejeniyar tsagaita bude wuta da aka cimma.(Safiyah Ma)














