Da misalin karfe 3 na yammacin ranar yau 4 ga Maris, an bude babban taron shekara-shekara na kwamitin kasa na majalisar ba da shawara kan harkokin siyasa ta kasar Sin (CPPCC) a babban dakin taron jama’a da ke birnin Beijing, inda shugaban kasar Sin Xi Jinping da sauran manyan jami’an gwamnati suka halarci bikin bude taron.
A yayin zaman taron na kwanaki bakwai, mambobin CPPCC za su saurari rahoton aiki na zaunannen kwamitin CPPCC da rahoton ayyukan samar da shawarwari, da halartar taron shekara-shekara na majalisar wakilan jama’ar kasar Sin (NPC) a matsayin wakilai marasa kuri’a, da saurare da kuma tattaunawa kan rahoton aikin gwamnati da sauran rahotannin da suka dace, kana da tattaunawa game da daftarin shirin shekaru biyar-biyar na bunkasa tattalin arzikin kasa da zamantakewar al’umma karo na 15.
Kwamitin kasa na babban taron majalisar ba da shawara kan harkokin siyasa na jama’ar kasar Sin (CPPCC) na da wa’adin aiki na shekaru biyar, kuma ya kan gudanar da cikakken zaman taron a kowace shekara. Taron bana shi ne karo na hudu na kwamitin CPPCC na 14. (Mai Fassara: Abdulrazaq Yahuza Jere)















Discussion about this post