An gudanar da bikin bude ofishin hedkwatar kungiyar raya tattalin arzikin kasashen yammacin Afirka (ECOWAS), wanda Sin ta taimaka wajen gina shi a birnin Abujan Nijeriya a jiya Alhamis.
Shugaban Saliyo, kuma shugaban kungiyar ECOWAS, kana shugaban kwamitin shugabannin gwamnatoci, Julius Maada Bio da mataimakin shugaban Najeriya Kashim Shettima da shugaban hukumar ECOWAS Omar Touray da jakadan Sin a Najeriya, kuma wakilin Sin a ECOWAS Yu Dunhai, sun halarci taron tare da gabatar da jawabai. Jami’ai sama da 400 da suka hada da wakilan kasashe mambobin ECOWAS da jakadun kasashen duniya a Najeriya da wakilan kamfanoni masu jarin kasar Sin dake Najeriya da ‘yan jarida ne suka halarci bikin.
A jawabinsa, jakada Yu Dunhai na Sin ya bayyana cewa, ginin ofishin hedkwatar ECOWAS da Sin ta ba da tallafin ginawa, wani babban aiki ne a karkashin tsarin dandalin hadin gwiwar Sin da Afirka, FOCAC, kuma abin koyi ne na hadin gwiwar kasashe masu tasowa a sabon zamani, wanda ke nuna zurfin abotar Sin da Afirka.
Ya ce bangaren Sin yana goyon bayan ECOWAS ta taka rawar gani a fannoni kamar kiyaye zaman lafiya a yankin da inganta ci gaban tattalin arziki, da kuma hadin gwiwa tare da kasashen Afirka wajen zamanintar da al’umma tare.
Wadanda suka yi jawabi daga bangaren Afirka sun nuna godiya ga gwamnatin Sin saboda goyon bayanta mai muhimmanci ga kasashen yammacin Afirka. Sun bayyana cewa, bude wannan gini a hukumance wani muhimmin tarihi ne na ci gaban ECOWAS, wanda zai taimaka wajen inganta hadewar yammacin Afirka da samun ci gaba da wadata. (Amina Xu)














