Mahukuntan Matatar Man Ɗangote, sun ƙaryata iƙirarin kamfanin dilalancin Mai na S&P Global na cewa, Ɗangote, na shigo da Man, daga ƙasar Lomé bayan Matatar ta fitar da shi, zuwa ƙasar ta Lome, inda take yin hada-hadar kasuwancinsa, a ƙara Togo.
A cewar Matatar ta Ɗangote, wannan iƙirarin na S&P Global, bai da wani tushe, ballanta wata makama, kuma an kitsa hakan ne, domin a kawai, a karkatar da kan jama’a.
“Wannan zargin kan Matatar, babu wasu bayanai, da suka goyi bayan iƙirarin, na cewar Matatar na hada-hadar Man a ƙasar Togo, “ Inji sanawar da mahukuntan Matatar suka fitar.
A cewar sanarwar, ɗaya daga cikin nauyin da ke a Matatar ta Ɗangote, shi ne, sarrafa Man da zai wadaci ƙasar, kuma Matatar za ta ci gaba da kasancewa, kan gaba wajen samar da Man a cikn ƙasar.
Sanarwar ta jaddda cewa, zargin Matatar na shigo da Man, ya saɓa ƙa’idar manufar da aka kafa Matatar ta Ɗangote.
A cewar mahukuntan, duk wani batu da ya shafi ɗaukacin kwangilar sayar da Man da duk wata yarjejeniya, ko kuma shigo da Man, mahukuntan Matatar, sun haramta yin hakan.
“Idan aka ƙiyasata tsadar kuɗaɗen da za a kashe wajen yin jigilar Man metric tan. daga Matatar Mai ta ƙasar Lomé, zuwa cikin ƙasar nan, tsadasr za ta kai zuwa dala 82.
“Matatar Man ta Ɗangote, ba ta yin ragi wajen shigo da Man, ballantana, ta cike giɓin tsadar kuɗin jigilar shigo da Man, cikin ƙasar nan ba, domin yin gasa kawai, ta ƙirƙiri tsadar Man a cikin kasuwannin sayar da Man, a cikin ƙasar
Sanawar ta ci gaba da cewa, babu wani mai Sarrafa mai da zai iya jurewa ciki giɓin tsadar yin jigilar Man domin shigoa da shi, zuwa cikin ƙasar.
Mahukuntan sun bayyana cewa, Matatar, na bin dukkanin ƙa’aidar da ta dace, wajen yin jigilar Man Matatar a zuwa cikin ƙasar nan.
Ta ƙara da cewa, ta bin wannan ƙa’idar ce, domin ta tabbatar da cewa, ta rabar da Man a ɗaukacin faɗin Nijeriya.
Sanarwar ta bayyana cewa, wannan iƙirarin na kamfanin S&P Global, ƙarya ce, tsagwaronta domin Matatar ta Ɗangote, na gudanar da ayyukanta ne, bisa ƙa’ida.
A cewar sanarwar, Matatar ta Ɗangote, ta kasance kan gaba a ƙasar nan, wajen yin gangamin rage yadda ake shigo da Man Fetur zuwa cikin Nijeriya.
Sanarwar ta yi nuni da cewa, barin ana shigo da Man cikin ƙasar nan, tamkar, daƙile ƙoƙarin sarrafa shi, a cikin ƙasar ne, wanda hakan kuma ke shafar kuɗaɗen ajiyar Gwamnatin ƙasar na ƙetare, tare da shafar kuɗaɗen musaya na Nijeriya.
Kazalika, sanarwar ta ce shigo da Man, zai kuma durƙurƙusar da ƙoƙarin manasana’atun sarrafa na cikin ƙasar nan.
“Babu ƙwaƙwarar hujja kan batun iƙirarin na kamfanin na S&P, kan cewar Matatar ta Ɗangote, na sake shigo da Man cikin Nijeriya.” Inji sanarwar.
Idan za a iya tunawa, babban jami’i a ɓangaren kula da makamashi a kamfanin na S&P Global, Matthew Tracey-Cook, ne, ya gabatar da wannan iƙirarin a jawabinsa a wajen taron da ƙungiyar Injiniyoyi ta ƙasa wato MEMAN.
Matthew yayi zargin cewa, dilalan Mai a ƙasar nan, na ƙara yawan shigo da Man da aka tace daga ƙetare, zuwa cikin Nijeriya, wanda kuma ya fito ne, daga Matatar Ɗangote, musamman daga ƙasar Lomé, inda ake hada-hadar sa, a ƙasar Togo.
Koda yake dai, Tracey-Cook, bai Ambato sunnan Matatar ta Ɗangote, wanda kuma Matatar ta Ɗangote, na da masaniyar hakan.
“Watanni da dama da suka wuce, musaman daga tsakanin Maris zuwa watan Yunin 2026, munga an shigo da Man da yawansa ya kai sama da kaso 70 zuwa 80, wanda kuma akasarinsa, ya fito ne, daga Matatar ta Ɗangote,” A cewarsa.
Jaridar PUNCH, ta ruwaito cewa, wasu daga cikin masu shigo da Man a watan Nuwambar 2025, sun zargi Matatar ta Ɗangote, kan sayar da Litocin Man da aka sake sarrawa, ga ƴan kasuwa a cikin ƙasar nan da Man, kan Naira 65 na kowacce Lita ɗaya.
Ƙungiyar ƴan Defon Man da kuma ƙungiyar masu sayar da Man ta ƙasa wato PPMAN da kuma sauran ƙananan masu sayar da man wato PROOAN suma a hirarar da ban da ban Jaridar Punch ta yi da su, sun tabbatar da wannan zargin.
“Matatar ta Ɗangote na sayar da Man ga ƴan kasuwa na ƙasa da ƙasa, kan farashin Naira 65 na kowacce Lita, saɓanin yadda Matatar, ke sayarwa ƴan kasuwa a cikin Nijeriya,” A cewarsu.
Hakan ne ya sanya babu ɗaya daga cikin ƴaƴan ƙungiyar mu, da zai iya sayen Man, daga Matatar ta Ɗangote.
Sun yi zargin cewa, idan Matatar ta Ɗangote ta sayawar da ƴan kasuwar na ƙasa da ƙasa, su kuma suna kai Man zuwa ƙasar Lomé, inda suke yin iƙirarin cewa, sun sayo ne da yawa.
Duk da cewa, Matatar ta Ɗangote, ta yi watsi da wannan zargin kan sayarwa da ƴan kasuwar na ƙasa da ƙasa Man kan farashi mai sauƙi a ƙasar Togo idan aka kwatanta kan farashin da take sayarwa a Nijeriya, wanda hakan, ya sanya ƴan Nijeriya ke ci gaba da tambaya menene ya sanya Matatar cikin ƙasar da ke tace Man, take sayar da shi, a ƙasar Togo.
Har zuwa yanzu dai, Matatar ta Ɗangote, akwai ƙarar da ta shigar a gaban kotu, kan buƙatar, a dakatar da shigo da Man ɗuwa cikin ƙasar nan, daga waje.














