A jiya Talata kwamitocin kula da harkokin bukukuwa na sassan yankin Hong Kong, suka gudanar da bikin bude aikace-aikacen taya murnar cika shekaru 29 da dawowar yankin Hong Kong kasar Sin, a babban dakin motsa jiki na yankin Hong Kong na kasar Sin, inda aka sanar da fara jerin bukukuwa bisa babban taken “Taya murnar cika shekaru 29, da dawo cikin kasa, da dukufa wajen neman sabon ci gaba”.
Kantoman yankin musamman na Hong Kong John Lee, ya gabatar da jawabi a yayin bikin, yana mai cewa gwamnatin yankin tana gaggauta tsara shirin shekaru biyar-biyar na bunkasa tattalin arziki, da zamantakewar yankin Hong Kong na 1, bisa bukatun shirin shekaru biyar-biyar na bunkasa tattalin arziki da zamantakewar kasar Sin na 15, ta yadda yankin Hong Kong zai halarci, da tallafa wa shirin bunkasa kasa yadda ya kamata. Haka zalika, gwamnatin yankin Hong Kong, za ta ci gaba da yin kirkire-kirkire, domin kyautata zamantakewar al’umma ta bai daya. (Mai Fassara: Maryam Yang)














