ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, July 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kwairanga Ya Kafa Tarihi A Shugabancin Hukumar Kula Da Kasuwar Hannun Jari Ta Nijeriya

by Shuaibu Shuaibu
11 hours ago
Tarihi

Kwazon Ndi Okereke-Onyuike, wacce ta kasance tsohuwar darakta janar ce ta hukumar da ke kula da kasuwar hannun jari ta Nijeriya kuma ta samu lambobin yabo da dama a kasar nan, ciki har da na Aliko Dangote, wanda a wani lokaci shi ne shugaban majalisar kasuwar jannun jari ta Nijeriya da Oscar Onyema, kwararre a kawo sauyi a shugabancin hukumar da ke kula da kasuwar hannun jari ta Nijeriya, ba karamin aiki ba ne.

Wannan shi ne abin da Umaru Kwairanga da Temi Popoola suke yi a matsayin shugaba da babban daraktan gudanarwa na rukunin musayar hannan jari a Nijeriya.

Hukumar gudanarwa ta kasuwar hannun jari ta Nijeriya ta yi fice a duniya. Sabbin bayanai daga binciken ‘Bloomberg’ na cewa kimanta musayar hannayen jari na duniya guda 92 a wannan shekara, sun nuna cewa kasuwar hannun jari ta Najeriya ta samu riba har kashi 67 cikin 100, wanda ya zarce na Kospi na Koriya ta Kudu, wanda ya zo na biyu da ribar kashi 66 cikin 100.

ADVERTISEMENT

Ribobin sun fi samuwa ne daga kamfanonin harkokin kudade. Amma ‘Bloomberg’ ta kuma danganta yadda kasuwar ta tashi da gyaran tattalin arziki, tsayayyen farashin mai, ingantaccen canjin kudin waje, inda naira ta kara daraja da kashi 4 cikin dari kan dala tun daga watan Janairu.

Kwairanga, wanda yake da shekaru 25 na kwarewa a aikin banki, fansho, zuba jari, da masana’antu kuma a baya ya yi aiki a matsayin mamba na majalisar musayar hannayen jari, an nada shi shugaban hukumar kala da kasuwar hannun jari ta Nijeriya a watan Oktoba, 2022.

LABARAI MASU NASABA

Yadda Kotun Daukaka Kara Ta Kama Hanyar Cin Gashin Kanta

Yadda NDLEA Ke Fatattakar Dillalan Miyagun Kwayoyi Na Kudancin Amurka

Yana cikin hukumar gudanarwa na kamfanin siminta na Ashaka da bankin Jaiz da kamfanin ‘Tangerine APT Pensions Limited’ da kamfanin FBN Senegal Limited, sannan kuma shi ne daraktan gudanarwa na Finmal Finance Serbices da wani banki na zuba jari.

Popoola, dan kasuwa a fannin harkokin zuba jari da aka horar a Wall Street, ya yi aiki a matsayin mai kula da kadarori a Landan da ke kasar Ingila a farkon aikinsa. Haka kuma, ya yi aiki a UBA, CSL Stokebrokers, sannan daga baya ya zama shugaban kamfanin ‘Renaissance Capital’. Ya zama shugaban rukunin rukunin musayar hannan jari ta Nijeriya a Janairu, 2024.

Hukumar karkashin jagorancin Kwairanga na samun ci gaba a kasuwar hannan jari da kuma bunkasan kamfanonin a Nijeriya a nan gaba kadan.

Kamfanin Airtel Africa PLC, a halin yanzu shi ne kamfani mafi daraja a kasuwr hannan jari da ke da naira tiriliyan 21.8, kusan dala biliyan 15.77. Amma a cikin manyan kamfanoni 10 mafi daraja a Afirka a shekarar 2025, babu wani kamfanin Nijeriya da ya shiga jerin. Biyu daga cikinsu na kasar Maroko ne, sauran duk suna Afirka ta Kudu.

Akwai kamfanonin sadarwa guda uku, cibiyoyin harkokin kudade guda hudu da kamfanonin hakar ma’adinai guda biyu. Naspers, kamfani fasahar sadarwa na kafar watsa labarai mai darajar kasuwar hannun jari ta dala biliyan 40 yana kan gaba.

Duk wannan zai canza ne da jerin wasu hannayen jarin matatar man Dangote a kasuwar hannun jari, wanda zai iya sa kasuwar ta zarce sauran kasuwanni a Nahiyar Afirka da ma duniya baki daya.

Ribarsa da tasirin sarrafa mai na cikin gida kan ma’aunin biyan kudi na kusan dukkan kasashen Afirka ba abin muhawara ba ne. Kuma yayin da masu zuwa jari ke neman cin moriyar saka babban matatar mai na Nahiyar Afirka a kasuwar hannun jari, haka nan ma mutane da ke kula da kasuwannin za su amfana.

Tarihi
Shuaibu Shuaibu
+ postsBio
  • Shuaibu Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/shuaibu-shuaibu/
    Yadda Kotun Daukaka Kara Ta Kama Hanyar Cin Gashin Kanta
  • Shuaibu Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/shuaibu-shuaibu/
    Yadda NDLEA Ke Fatattakar Dillalan Miyagun Kwayoyi Na Kudancin Amurka
  • Shuaibu Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/shuaibu-shuaibu/
    Gwamnan Da Bai Taba Samun Mulkin Jihar Kano Ba
  • Shuaibu Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/shuaibu-shuaibu/
    Ibrahim Aliyu Na Ci Gaba Da Rasa Tasiri A Harkar Fili Da Gidaje A Yankin Abuja

MASU ALAKA

Yadda Kotun Daukaka Kara Ta Kama Hanyar Cin Gashin Kanta
Bakon Marubuci

Yadda Kotun Daukaka Kara Ta Kama Hanyar Cin Gashin Kanta

July 24, 2026
Yadda NDLEA Ke Fatattakar Dillalan Miyagun Kwayoyi Na Kudancin Amurka
Bakon Marubuci

Yadda NDLEA Ke Fatattakar Dillalan Miyagun Kwayoyi Na Kudancin Amurka

July 17, 2026
Gwamnan Da Bai Taba Samun Mulkin Jihar Kano Ba
Bakon Marubuci

Gwamnan Da Bai Taba Samun Mulkin Jihar Kano Ba

July 17, 2026
Next Post
Sin Tana Son More Damammakin Fasahar AI a Maimakon Babakere a Wannan Bangare Da Kasashen Yamma Suka Dade Suna Yi

Sin Tana Son More Damammakin Fasahar AI a Maimakon Babakere a Wannan Bangare Da Kasashen Yamma Suka Dade Suna Yi

LABARAI MASU NASABA

An Karrama Masana Ilimin Lissafi Na Kasar Sin Da Lambobin Yabo Na Fields Medal

An Karrama Masana Ilimin Lissafi Na Kasar Sin Da Lambobin Yabo Na Fields Medal

July 24, 2026
Ta Da Zaune Tsaye Da Philippines Ta Yi A Teku Ba Zai Lalata Dangantakar Hadin Gwiwar Sin Da ASEAN Ba

Ta Da Zaune Tsaye Da Philippines Ta Yi A Teku Ba Zai Lalata Dangantakar Hadin Gwiwar Sin Da ASEAN Ba

July 24, 2026
Jadawalin INEC:Kotun Daukaka Kara Ta Kassara Fatan Jam’iyyu Da ‘Yan Siyasa

Jadawalin INEC:Kotun Daukaka Kara Ta Kassara Fatan Jam’iyyu Da ‘Yan Siyasa

July 24, 2026
An Zartas Da Sanarwar Chengdu A Taron Ministocin Kungiyar APEC Kan Harkar Raya Fasahohin Dijital Da AI

An Zartas Da Sanarwar Chengdu A Taron Ministocin Kungiyar APEC Kan Harkar Raya Fasahohin Dijital Da AI

July 24, 2026
NNPP Za Ta Kwace Mulki A Jihar Imo – Kwankwaso

Jam’iyyar NDC Ta Shirya Tsaf Domin Kafa Gwamnati A 2027 —Kwankwaso

July 24, 2026
Sin Ta Kara Kamfanoni 14 Na Tarayyar Turai Cikin Jerin Wadanda Aka Hana Fitar Masu Da Kaya

Sin Ta Kara Kamfanoni 14 Na Tarayyar Turai Cikin Jerin Wadanda Aka Hana Fitar Masu Da Kaya

July 24, 2026
Kashim Shettima Ya Mayar Da Martani Kan Tsadar Rayuwa

Kyamar Baki: Shettima Ya Ja Kunnen Gwamnatin Afirka Ta Kudu

July 24, 2026
Yadda Kasar Sin Ta Samar Da Ci Gaba Na Bai Daya

Yadda Kasar Sin Ta Samar Da Ci Gaba Na Bai Daya

July 24, 2026
Hatsin Da Kasar Sin Ta Girbe Da Lokacin Zafin Bana Ya Zarce Tan Miliyan 150

Hatsin Da Kasar Sin Ta Girbe Da Lokacin Zafin Bana Ya Zarce Tan Miliyan 150

July 24, 2026
Wani Dalilin Da Ya Sa Al’Ummar Afirka Ke Kaunar Kasar Sin Shi Ne Yadda Take Kokarin Zuba Musu Jari

Wani Dalilin Da Ya Sa Al’Ummar Afirka Ke Kaunar Kasar Sin Shi Ne Yadda Take Kokarin Zuba Musu Jari

July 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.