ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kwairanga Ya Kafa Tarihi A Shugabancin Hukumar Kula Da Kasuwar Hannun Jari Ta Nijeriya

by Shuaibu Shuaibu
2 months ago
Tarihi

Kwazon Ndi Okereke-Onyuike, wacce ta kasance tsohuwar darakta janar ce ta hukumar da ke kula da kasuwar hannun jari ta Nijeriya kuma ta samu lambobin yabo da dama a kasar nan, ciki har da na Aliko Dangote, wanda a wani lokaci shi ne shugaban majalisar kasuwar jannun jari ta Nijeriya da Oscar Onyema, kwararre a kawo sauyi a shugabancin hukumar da ke kula da kasuwar hannun jari ta Nijeriya, ba karamin aiki ba ne.

Wannan shi ne abin da Umaru Kwairanga da Temi Popoola suke yi a matsayin shugaba da babban daraktan gudanarwa na rukunin musayar hannan jari a Nijeriya.

Hukumar gudanarwa ta kasuwar hannun jari ta Nijeriya ta yi fice a duniya. Sabbin bayanai daga binciken ‘Bloomberg’ na cewa kimanta musayar hannayen jari na duniya guda 92 a wannan shekara, sun nuna cewa kasuwar hannun jari ta Najeriya ta samu riba har kashi 67 cikin 100, wanda ya zarce na Kospi na Koriya ta Kudu, wanda ya zo na biyu da ribar kashi 66 cikin 100.

ADVERTISEMENT

Ribobin sun fi samuwa ne daga kamfanonin harkokin kudade. Amma ‘Bloomberg’ ta kuma danganta yadda kasuwar ta tashi da gyaran tattalin arziki, tsayayyen farashin mai, ingantaccen canjin kudin waje, inda naira ta kara daraja da kashi 4 cikin dari kan dala tun daga watan Janairu.

Kwairanga, wanda yake da shekaru 25 na kwarewa a aikin banki, fansho, zuba jari, da masana’antu kuma a baya ya yi aiki a matsayin mamba na majalisar musayar hannayen jari, an nada shi shugaban hukumar kala da kasuwar hannun jari ta Nijeriya a watan Oktoba, 2022.

LABARAI MASU NASABA

Buni Ya Nuna Kwarewarsa Ta Diflomasiyya

Shin Tinubu Ya Tabbatar Da Sauke Ribadu Daga Mukaminsa?

Yana cikin hukumar gudanarwa na kamfanin siminta na Ashaka da bankin Jaiz da kamfanin ‘Tangerine APT Pensions Limited’ da kamfanin FBN Senegal Limited, sannan kuma shi ne daraktan gudanarwa na Finmal Finance Serbices da wani banki na zuba jari.

Popoola, dan kasuwa a fannin harkokin zuba jari da aka horar a Wall Street, ya yi aiki a matsayin mai kula da kadarori a Landan da ke kasar Ingila a farkon aikinsa. Haka kuma, ya yi aiki a UBA, CSL Stokebrokers, sannan daga baya ya zama shugaban kamfanin ‘Renaissance Capital’. Ya zama shugaban rukunin rukunin musayar hannan jari ta Nijeriya a Janairu, 2024.

Hukumar karkashin jagorancin Kwairanga na samun ci gaba a kasuwar hannan jari da kuma bunkasan kamfanonin a Nijeriya a nan gaba kadan.

Kamfanin Airtel Africa PLC, a halin yanzu shi ne kamfani mafi daraja a kasuwr hannan jari da ke da naira tiriliyan 21.8, kusan dala biliyan 15.77. Amma a cikin manyan kamfanoni 10 mafi daraja a Afirka a shekarar 2025, babu wani kamfanin Nijeriya da ya shiga jerin. Biyu daga cikinsu na kasar Maroko ne, sauran duk suna Afirka ta Kudu.

Akwai kamfanonin sadarwa guda uku, cibiyoyin harkokin kudade guda hudu da kamfanonin hakar ma’adinai guda biyu. Naspers, kamfani fasahar sadarwa na kafar watsa labarai mai darajar kasuwar hannun jari ta dala biliyan 40 yana kan gaba.

Duk wannan zai canza ne da jerin wasu hannayen jarin matatar man Dangote a kasuwar hannun jari, wanda zai iya sa kasuwar ta zarce sauran kasuwanni a Nahiyar Afirka da ma duniya baki daya.

Ribarsa da tasirin sarrafa mai na cikin gida kan ma’aunin biyan kudi na kusan dukkan kasashen Afirka ba abin muhawara ba ne. Kuma yayin da masu zuwa jari ke neman cin moriyar saka babban matatar mai na Nahiyar Afirka a kasuwar hannun jari, haka nan ma mutane da ke kula da kasuwannin za su amfana.

Tarihi
Shuaibu Shuaibu
+ postsBio
  • Shuaibu Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/shuaibu-shuaibu/
    Buni Ya Nuna Kwarewarsa Ta Diflomasiyya
  • Shuaibu Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/shuaibu-shuaibu/
    Shin Tinubu Ya Tabbatar Da Sauke Ribadu Daga Mukaminsa?
  • Shuaibu Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/shuaibu-shuaibu/
    Akwai Ayar Tabaya Kan Zuba Hannun Jarin Dala Miliyan 750 Na Yari
  • Shuaibu Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/shuaibu-shuaibu/
    Wa Tanimu Turaki Ke Fafutukar Karewa?

MASU ALAKA

Zanga-Zanga: Gwamnatin Yobe Ta Bayar Da Umarnin Rufe Makarantun Jihar
Bakon Marubuci

Buni Ya Nuna Kwarewarsa Ta Diflomasiyya

August 28, 2026
An Kusa Ceto Ɗaliban Neja Da Aka Sace – Ribadu
Bakon Marubuci

Shin Tinubu Ya Tabbatar Da Sauke Ribadu Daga Mukaminsa?

August 28, 2026
Yadda Kotun Daukaka Kara Ta Kama Hanyar Cin Gashin Kanta
Bakon Marubuci

Yadda Kotun Daukaka Kara Ta Kama Hanyar Cin Gashin Kanta

July 24, 2026
Next Post
Sin Tana Son More Damammakin Fasahar AI a Maimakon Babakere a Wannan Bangare Da Kasashen Yamma Suka Dade Suna Yi

Sin Tana Son More Damammakin Fasahar AI a Maimakon Babakere a Wannan Bangare Da Kasashen Yamma Suka Dade Suna Yi

LABARAI MASU NASABA

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

September 8, 2026
Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja

Kano Za Ta Kafa Sansanonin Sojoji A Ƙananan Hukumomin Da Ke Fuskantar Barazanar Tsaro

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.