Mai magana da yawun ma’aikatar harkokin wajen kasar Sin Guo Jiakun ya bayyana a yau Talata cewa, ya zuwa yanzu, an gudanar da kusan ayyuka daban-daban har 500 masu ban sha’awa a cikin shekarar bana ta cudanyar jama’a da musanyar al’adu tsakanin Sin da Afirka, wadanda ke nuna manyan siffofi guda uku da suka hada da yawan fitattun abubuwa, cikakkun fannoni, da kuma shigar jama’a mai dimbin yawa.
Guo Jiakun ya bayyana haka ne a yayin taron manema labarai na yau da kullum da aka yi a wannan rana, inda ya kara da cewa, shekarar 2026 shekara ce ta cudanyar jama’a da musanyar al’adu tsakanin Sin da Afirka.
Wannan ne kuma muhimmin ra’ayin bai daya da shugaban kasar Sin Xi Jinping ya cimma tare da shugabannin kasashen Afirka, da nufin kara inganta sada zumunta, da karfafa yin mu’amala da hadin kai tsakanin Sin da Afirka.
Baya ga haka, Guo Jiakun ya ce, kashi na biyu na ayyukan na wannan shekarar za su fi kayatarwa, kuma za a fara su nan ba da jimawa ba.
Ya ce kasar Sin na son hada hannu da bangaren Afirka, don gudanar da dukkan ayyukan yadda ya kamata, da zurfafa hadin gwiwar sassan biyu ta fannin cudanyar jama’a da musanyar al’adu, tare kuma da samar da sabon kuzari ga inganta raya al’umma mai kyakkyawar makoma ta bai daya ga Sin da Afirka a ko da yaushe cikin ko wane yanayi a sabon zamani. (Bilkisu Xin)














