ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Sunday, July 5, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tinubu Ya Shimfiɗa Wa Arewacin Nijeriya Ayyuka Sama Da Kowane Shugaban Ƙasa – Uba Sani

by Sadiq
5 days ago

Gwamnan Jihar Kaduna, Uba Sani, ya ce Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya aiwatar da ayyukan ci gaba a Arewacin Nijeriya sama da duk wani shugaban ƙasa da ya gabace shi.

Ya bayyana haka ne yayin wata hira da gidan talabijin na ARISE a daren ranar Talata.Uba Sani ya ce masu hasashen cewa Arewa ba za ta goyi bayan Tinubu a zaɓen 2027 ba, ba su yi la’akari da ayyukan da gwamnatinsa ta aiwatar ba.

Ya bayyana cewa yana da tabbacin Tinubu zai samu ƙuri’u a Arewa sama da waɗanda ya samu a zaɓen shugaban ƙasa na 2023.

ADVERTISEMENT

Gwamnan ya ce Gwamnatin Tarayya ta samu gagarumin ci gaba wajen aikin hanyar Abuja zuwa Kaduna, inda ya bayyana cewa an riga an biya ‘yan kwangila sama da naira biliyan 600.

Ya ƙara da cewa ana sa ran za a kammala aikin tare da ƙaddamar da shi a watan Nuwamba.

LABARAI MASU NASABA

Jam’iyyar PDP Ce Za Ta Dawo Da Kwanciyar Hankali A Nijeriya – Hajiya Khadija

Atiku Ya Naɗa Kenneth Okonkwo A Matsayin Kakakin Yaƙin Neman Zaɓensa

Haka kuma, ya ce an ci gaba da aikin hanyar Kaduna zuwa Birnin Gwari bayan watsi da aikin tsawon shekaru masu yawa, inda aka riga aka saki wani ɓangare na kuɗin aikin da ya kai naira biliyan 178.

Uba Sani ya kuma ce Jihar Kaduna ta amfana da tallafin Gwamnatin Tarayya a fannin noma na shirin SAPZ da kuma rabon takin zamani ga ƙananan manoma.

Ya ƙara da cewa gwamnatin Tinubu ta amince da kafa Jami’ar Kimiyya da Fasaha ta Tarayya a Kudancin Kaduna, ta mayar da ɗaya daga cikin asibitocin jihar zuwa Cibiyar Kiwon Lafiya ta Tarayya, sannan ta amince da aikin titin jirgin ƙasa a cikin Kaduna da kuɗinsa ya kai naira tiriliyan ɗaya.

A cewarsa, waɗannan ayyuka sun inganta rayuwar al’ummar jihar kuma sun nuna ƙudirin gwamnatin Tinubu na samar wa Arewacin Nijeriya ci gaba.

Ya ce hakan zai sa shugaban ƙasar ya ƙara samun goyon baya daga yankin a zaɓen 2027.

MASU ALAKA

Jam’iyyar PDP Ce Za Ta Dawo Da Kwanciyar Hankali A Nijeriya – Hajiya Khadija
Siyasa

Jam’iyyar PDP Ce Za Ta Dawo Da Kwanciyar Hankali A Nijeriya – Hajiya Khadija

July 5, 2026
Atiku
Siyasa

Atiku Ya Naɗa Kenneth Okonkwo A Matsayin Kakakin Yaƙin Neman Zaɓensa

July 2, 2026
‘Yan Adawa Sun Mayar Da Matsalar Tsaro Siyasa – Yusuf Gagdi
Manyan Labarai

‘Yan Adawa Sun Mayar Da Matsalar Tsaro Siyasa – Yusuf Gagdi

July 1, 2026
Next Post
An Gudanar Da Taron Murnar Cika Shekaru 105 Da Kafuwar Jam’iyyar Kwaminis Ta Sin

An Gudanar Da Taron Murnar Cika Shekaru 105 Da Kafuwar Jam'iyyar Kwaminis Ta Sin

LABARAI MASU NASABA

Ko Kafa Ƴansandan Jihohi Zai Taimaka Wajen Kawo Ƙarshen Matsalolin Tsaro?

Ko Kafa Ƴansandan Jihohi Zai Taimaka Wajen Kawo Ƙarshen Matsalolin Tsaro?

July 5, 2026
Rashin Tarbiyya Da Ilimin Addini Ne Ke Sa Matasa Ɗaukar Doka a Hannu – Hon. Aminu Adam

Rashin Tarbiyya Da Ilimin Addini Ne Ke Sa Matasa Ɗaukar Doka a Hannu – Hon. Aminu Adam

July 5, 2026
Kayayyakin Sin Sun Jawo Hankalin Sassan Kasa Da Kasa

Kayayyakin Sin Sun Jawo Hankalin Sassan Kasa Da Kasa

July 5, 2026
Sin Da Rasha Za Su Gudanar Da Atisayen Sojojin Ruwa Da Sintiri Na Hadin Gwiwa

Sin Da Rasha Za Su Gudanar Da Atisayen Sojojin Ruwa Da Sintiri Na Hadin Gwiwa

July 5, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Yi Allah-Wadai Da Kisan ‘Ƴan Nijeriya 2 A Afrika Ta Kudu

Gwamnatin Tarayya Ta Yi Allah-Wadai Da Kisan ‘Ƴan Nijeriya 2 A Afrika Ta Kudu

July 5, 2026
Tawagar Jami’an Lafiya Ta Sin Ta Kafa Cibiyar Horar Da Ma’aikatan Jinya A Saliyo

Tawagar Jami’an Lafiya Ta Sin Ta Kafa Cibiyar Horar Da Ma’aikatan Jinya A Saliyo

July 5, 2026
Nasiha Ga Uwargida Kan Zafin Kishi (2)

Nasiha Ga Uwargida Kan Zafin Kishi (2)

July 5, 2026
Sin Ta Sha Alwashin Karfafa Musaya Da Sweden A Dukkanin Fannoni

Sin Ta Sha Alwashin Karfafa Musaya Da Sweden A Dukkanin Fannoni

July 5, 2026
Messi Da Mbappé Na Jagorantar Cin Ƙwallaye A Gasar Kofin Duniya

Messi Da Mbappé Na Jagorantar Cin Ƙwallaye A Gasar Kofin Duniya

July 5, 2026
Adadin Mutanen Da Tsananin Zafi Ya Kashe A Turai Ya Haura Dubu 1,300 —WHO

Adadin Mutanen Da Tsananin Zafi Ya Kashe A Turai Ya Haura Dubu 1,300 —WHO

July 5, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.