Gwamnan Jihar Kaduna, Uba Sani, ya ce Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya aiwatar da ayyukan ci gaba a Arewacin Nijeriya sama da duk wani shugaban ƙasa da ya gabace shi.
Ya bayyana haka ne yayin wata hira da gidan talabijin na ARISE a daren ranar Talata.Uba Sani ya ce masu hasashen cewa Arewa ba za ta goyi bayan Tinubu a zaɓen 2027 ba, ba su yi la’akari da ayyukan da gwamnatinsa ta aiwatar ba.
Ya bayyana cewa yana da tabbacin Tinubu zai samu ƙuri’u a Arewa sama da waɗanda ya samu a zaɓen shugaban ƙasa na 2023.
Gwamnan ya ce Gwamnatin Tarayya ta samu gagarumin ci gaba wajen aikin hanyar Abuja zuwa Kaduna, inda ya bayyana cewa an riga an biya ‘yan kwangila sama da naira biliyan 600.
Ya ƙara da cewa ana sa ran za a kammala aikin tare da ƙaddamar da shi a watan Nuwamba.
Haka kuma, ya ce an ci gaba da aikin hanyar Kaduna zuwa Birnin Gwari bayan watsi da aikin tsawon shekaru masu yawa, inda aka riga aka saki wani ɓangare na kuɗin aikin da ya kai naira biliyan 178.
Uba Sani ya kuma ce Jihar Kaduna ta amfana da tallafin Gwamnatin Tarayya a fannin noma na shirin SAPZ da kuma rabon takin zamani ga ƙananan manoma.
Ya ƙara da cewa gwamnatin Tinubu ta amince da kafa Jami’ar Kimiyya da Fasaha ta Tarayya a Kudancin Kaduna, ta mayar da ɗaya daga cikin asibitocin jihar zuwa Cibiyar Kiwon Lafiya ta Tarayya, sannan ta amince da aikin titin jirgin ƙasa a cikin Kaduna da kuɗinsa ya kai naira tiriliyan ɗaya.
A cewarsa, waɗannan ayyuka sun inganta rayuwar al’ummar jihar kuma sun nuna ƙudirin gwamnatin Tinubu na samar wa Arewacin Nijeriya ci gaba.
Ya ce hakan zai sa shugaban ƙasar ya ƙara samun goyon baya daga yankin a zaɓen 2027.














