ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Sunday, July 26, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tinubu Ya Shimfiɗa Wa Arewacin Nijeriya Ayyuka Sama Da Kowane Shugaban Ƙasa – Uba Sani

by Sadiq
4 weeks ago

Gwamnan Jihar Kaduna, Uba Sani, ya ce Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya aiwatar da ayyukan ci gaba a Arewacin Nijeriya sama da duk wani shugaban ƙasa da ya gabace shi.

Ya bayyana haka ne yayin wata hira da gidan talabijin na ARISE a daren ranar Talata.Uba Sani ya ce masu hasashen cewa Arewa ba za ta goyi bayan Tinubu a zaɓen 2027 ba, ba su yi la’akari da ayyukan da gwamnatinsa ta aiwatar ba.

Ya bayyana cewa yana da tabbacin Tinubu zai samu ƙuri’u a Arewa sama da waɗanda ya samu a zaɓen shugaban ƙasa na 2023.

ADVERTISEMENT

Gwamnan ya ce Gwamnatin Tarayya ta samu gagarumin ci gaba wajen aikin hanyar Abuja zuwa Kaduna, inda ya bayyana cewa an riga an biya ‘yan kwangila sama da naira biliyan 600.

Ya ƙara da cewa ana sa ran za a kammala aikin tare da ƙaddamar da shi a watan Nuwamba.

LABARAI MASU NASABA

2027: Magoya Bayan Tinubu Sun Yi Watsi Da Sukar Takarar Musulmi-Musulmi Da Kwankwaso Ya Yi

Kabiru Gaya Ya Amince Zai Sauya Sheƙa Zuwa APC

Haka kuma, ya ce an ci gaba da aikin hanyar Kaduna zuwa Birnin Gwari bayan watsi da aikin tsawon shekaru masu yawa, inda aka riga aka saki wani ɓangare na kuɗin aikin da ya kai naira biliyan 178.

Uba Sani ya kuma ce Jihar Kaduna ta amfana da tallafin Gwamnatin Tarayya a fannin noma na shirin SAPZ da kuma rabon takin zamani ga ƙananan manoma.

Ya ƙara da cewa gwamnatin Tinubu ta amince da kafa Jami’ar Kimiyya da Fasaha ta Tarayya a Kudancin Kaduna, ta mayar da ɗaya daga cikin asibitocin jihar zuwa Cibiyar Kiwon Lafiya ta Tarayya, sannan ta amince da aikin titin jirgin ƙasa a cikin Kaduna da kuɗinsa ya kai naira tiriliyan ɗaya.

A cewarsa, waɗannan ayyuka sun inganta rayuwar al’ummar jihar kuma sun nuna ƙudirin gwamnatin Tinubu na samar wa Arewacin Nijeriya ci gaba.

Ya ce hakan zai sa shugaban ƙasar ya ƙara samun goyon baya daga yankin a zaɓen 2027.

MASU ALAKA

Kwankwaso Zai Koma ADC Ranar Litinin
Manyan Labarai

2027: Magoya Bayan Tinubu Sun Yi Watsi Da Sukar Takarar Musulmi-Musulmi Da Kwankwaso Ya Yi

July 22, 2026
Kabiru Gaya Ya Amince Zai Sauya Sheƙa Zuwa APC
Labarai

Kabiru Gaya Ya Amince Zai Sauya Sheƙa Zuwa APC

July 21, 2026
Gwamnatin Tarayya Na Biyan Tallafin Man Fetur A Asirce – El-Rufai
Siyasa

Ba Zan Iya Jure Halayen El-Rufai Ba Shi Yasa Na Fice Daga ADC – Salihu Lukman

July 16, 2026
Next Post
An Gudanar Da Taron Murnar Cika Shekaru 105 Da Kafuwar Jam’iyyar Kwaminis Ta Sin

An Gudanar Da Taron Murnar Cika Shekaru 105 Da Kafuwar Jam'iyyar Kwaminis Ta Sin

LABARAI MASU NASABA

Shugaban Senegal Ya Jinjinawa Kasar Sin Bisa Taimakon Gina Zaurukan Gudanar Da Wasannin Gasar Olympics Ta Matasa

Shugaban Senegal Ya Jinjinawa Kasar Sin Bisa Taimakon Gina Zaurukan Gudanar Da Wasannin Gasar Olympics Ta Matasa

July 26, 2026

Ƴan Bindiga Sun Yi Garkuwa Da Alƙalin Babbar Kotu A Kebbi

July 26, 2026
Bala Mohammed

Sadakin Budurwa ₦3,000 Na Bazawara ₦1,500: Gwamnatin Bauchi Ta Ƙaryata Batun

July 26, 2026
Arewa Ta Rasa Alƙiblarta – Dattawan Arewa

Arewa Ta Rasa Alƙiblarta – Dattawan Arewa

July 26, 2026
Dauda Dauda Lawal Ya Sha Alwashin Farfaɗo Da Masana’antar Yadi Ta Zamfara

Dauda Dauda Lawal Ya Sha Alwashin Farfaɗo Da Masana’antar Yadi Ta Zamfara

July 26, 2026
Gwamna Uba Sani Ya Ƙaddamar Da Rabon Taki Kyauta Ga Manoma 150,000  A Kaduna

Gwamna Uba Sani Ya Ƙaddamar Da Rabon Taki Kyauta Ga Manoma 150,000 A Kaduna

July 26, 2026
Shugaban Kasa Yana Bibiyar Zanga-zangar Matsin Rayuwa – Minista

Birtaniya Ta Yaba Wa Tinubu Kan Sauye-sauyen Tattalin Arziki

July 25, 2026
Ofishin Jakadancin Sin A Nijeriya Ya Shirya Taron Murnar Cika Shekaru 99 Da Kafuwar Rundunar PLA Ta Sin

Ofishin Jakadancin Sin A Nijeriya Ya Shirya Taron Murnar Cika Shekaru 99 Da Kafuwar Rundunar PLA Ta Sin

July 25, 2026
Sabon Rahoton Bankin Duniya Ya Yaba Da Yadda Tattalin Arzkin Nijeriya Ke Bunkasa

Sabon Rahoton Bankin Duniya Ya Yaba Da Yadda Tattalin Arzkin Nijeriya Ke Bunkasa

July 25, 2026
Farfesa Dr. Otto Heinrich Herzog: Sin Tana Da Tsari Mai Kyau Na Aiwatar Da Dabarun Ci Gaba

Farfesa Dr. Otto Heinrich Herzog: Sin Tana Da Tsari Mai Kyau Na Aiwatar Da Dabarun Ci Gaba

July 25, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.