Gwamnatin Jihar Katsina ta fara rarraba keken adaidait guda 238 zuwa cibiyoyin kula da lafiya matakin farko a faɗin jihar, domin inganta kai marasa lafiya zuwa asibitoci musamman a yankunan karkara.
Ministan Kiwon Lafiya da Jin Daɗin Jama’a mai kula da harkokin ma’aikatar, Farfesa Muhammad Ali Pate, ne ya ƙaddamar da motocin a ranar Talata a Katsina.
Motocin 238 da aka ƙaddamar su ne kashi na farko daga cikin 361 da aka shirya samarwa jihar, inda ake sa ran kowace daga cikin gundumomi 361 na jihar za ta samu keke guda domin tallafa wa harkokin lafiya a matakin farko.
Haka kuma, jihar ta ƙaddamar da motocin ɗaukar marasa lafiya 18 masu cikakken kayan tallafin rayuwa (Advanced Life Support), bayan Gwamnatin Tarayya ta ƙara mata wasu motoci uku.
Gwamnatin jihar ta ce samar da motocin na daga cikin matakan ƙarfafa tsarin kula da lafiya a matakin farko da kuma sauƙaƙa wa al’umma, musamman mazauna karkara, samun damar zuwa asibitoci cikin gaggawa.














