ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Tuesday, September 15, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnatin Sakkwato Ta Rufe Masallacin Sheikh Lukuwa Bayan Harin Da Aka Kai Masa

by Sadiq
47 minutes ago

Gwamnatin Jihar Sakkwato ta bayar da umarnin rufe Masallacin Juma’a na Sheikh Musa Lukuwa da ke Mabera, bayan da wani matashi ya caka masa wuƙa jim kaɗan bayan idar da Sallar Juma’a a makon da ya gabata.

Gwamnatin ta kuma umarci a gudanar da cikakken bincike a kan lamarin, tare da ayyana masallacin a matsayin wurin da ake gudanar da binciken manyan laifuka har sai an fitar da sabon umarni.

Rahotanni sun ce wani matashi da ke cikin masu salla ya kai wa Sheikh Lukuwa hari da wuƙa jim kaɗan bayan idar da Sallar Juma’a.

ADVERTISEMENT

An ce matashin ya yi masa rauni a wuya da hannun hagu.

Sauran masu masallata sun cafke wanda ake zargin, inda suka lakaɗa masa dukan da ya yi sanadin ajalinsa kafin jami’an tsaro su isa wajen.

LABARAI MASU NASABA

’Yan Ta’adda Na Shirin Kai Hare-Hare Makarantu, Wuraren Ibada Da Sansanonin NYSC – ’Yansanda

Hannun Jari: Dangote Ya Yi Wa ’Yan Nijeriya Alƙawarin Samun Gaggwaɓar Riba

’Yansanda sun tabbatar da cewa mutum ɗaya ya rasu sakamakon rikicin.

An garzaya da Sheikh Lukuwa zuwa asibiti domin kula da shi.

Daga baya, kakakin ’yansandan jihar, DSP Ahmad Rufa’i, ya ce an sallame shi bayan likitoci sun kula da lafiyarsa.

Shi ma malamin ya bayyana cewa yana cikin ƙoshin lafiya tare da kira ga mabiyansa da jama’a su kwantar da hankalinsu.

Lamarin ya haifar da tashin hankali a wasu sassan birnin Sakkwato, ciki har da Sahara, Bello Way da Aliyu Jodi.

Wasu ’yan kasuwa sun rufe shaguna na ɗan lokaci saboda fargabar ɓarkewar rikici, yayin da jami’an tsaro suka mamaye muhimman wurare domin tabbatar da zaman lafiya.

Wasu rahotanni sun danganta harin da wata tsohuwar magana da Sheikh Lukuwa ya yi a wani wa’azinsa, wadda ta jawo ce-ce-ku-ce da barazana a baya.

An kuma ruwaito cewa malamin da wasu mabiyansa sun kai ƙorafi ga gwamnatin jihar kwanaki kaɗan kafin harin, inda suka nuna damuwa kan barazanar da suke fuskanta.

Sai dai ’yansanda suna bincike domin gano ainihin abin da ya jawo harin.

’Yansanda sun yi kira ga jama’a da su kwantar da hankalinsu, su guji ɗaukar doka a hannunsu, tare da barin hukumomi su gudanar da bincike a kan lamarin.

MASU ALAKA

Wani Mutum Ya Kashe Kishiyar Mahaifiyarsa A Kogi
Manyan Labarai

’Yan Ta’adda Na Shirin Kai Hare-Hare Makarantu, Wuraren Ibada Da Sansanonin NYSC – ’Yansanda

September 15, 2026
Hannun Jari: Dangote Ya Yi Wa ’Yan Nijeriya Alƙawarin Samun Gaggwaɓar Riba
Manyan Labarai

Hannun Jari: Dangote Ya Yi Wa ’Yan Nijeriya Alƙawarin Samun Gaggwaɓar Riba

September 15, 2026
Dangote Ya Sake Zama Wanda Ya Fi Kowa Kudi A Afrika Karo Na 12
Manyan Labarai

Arziƙin Dangote Ya Haura Dala Biliyan 50 Bayan Fara Sayar Da Hannun Jarin Matatarsa – Forbes

September 15, 2026
Next Post
Wani Mutum Ya Kashe Kishiyar Mahaifiyarsa A Kogi

’Yan Ta’adda Na Shirin Kai Hare-Hare Makarantu, Wuraren Ibada Da Sansanonin NYSC – ’Yansanda

LABARAI MASU NASABA

Wani Mutum Ya Kashe Kishiyar Mahaifiyarsa A Kogi

’Yan Ta’adda Na Shirin Kai Hare-Hare Makarantu, Wuraren Ibada Da Sansanonin NYSC – ’Yansanda

September 15, 2026
Gwamnatin Sakkwato Ta Rufe Masallacin Sheikh Lukuwa Bayan Harin Da Aka Kai Masa

Gwamnatin Sakkwato Ta Rufe Masallacin Sheikh Lukuwa Bayan Harin Da Aka Kai Masa

September 15, 2026
Hannun Jari: Dangote Ya Yi Wa ’Yan Nijeriya Alƙawarin Samun Gaggwaɓar Riba

Hannun Jari: Dangote Ya Yi Wa ’Yan Nijeriya Alƙawarin Samun Gaggwaɓar Riba

September 15, 2026
Dangote Ya Sake Zama Wanda Ya Fi Kowa Kudi A Afrika Karo Na 12

Arziƙin Dangote Ya Haura Dala Biliyan 50 Bayan Fara Sayar Da Hannun Jarin Matatarsa – Forbes

September 15, 2026
Jawabin Xi A Taron BRICS, Mafita Ce Ga Matsalolin Duniya

Jawabin Xi A Taron BRICS, Mafita Ce Ga Matsalolin Duniya

September 14, 2026
Duk Wani Yunkuri Na Karfafa Burin Japan Na Fadada Karfin Soji Zai Jefa Yankin Cikin Hadari

Duk Wani Yunkuri Na Karfafa Burin Japan Na Fadada Karfin Soji Zai Jefa Yankin Cikin Hadari

September 14, 2026
Tsohon Firaminsitan Jordan: Kasar Sin Tana Kan Gaba Wajen Gudanar Da Fasahar AI A Duniya

Tsohon Firaminsitan Jordan: Kasar Sin Tana Kan Gaba Wajen Gudanar Da Fasahar AI A Duniya

September 14, 2026
Hadin Gwiwar BRICS Na Jagorantar Hadin Kan Kasashe Masu Tasowa Da Dogaro Da Karfin Kansu

Hadin Gwiwar BRICS Na Jagorantar Hadin Kan Kasashe Masu Tasowa Da Dogaro Da Karfin Kansu

September 14, 2026
Na Miƙa Kaina Ga Hukumomin Tsaro – Sanata Shehu Buba

Na Miƙa Kaina Ga Hukumomin Tsaro – Sanata Shehu Buba

September 14, 2026
Sin Na Shirin Fadada Samar Da Hidimomin Reno Da Na Kiwon Lafiyar Yara Masu Rahusa

Sin Na Shirin Fadada Samar Da Hidimomin Reno Da Na Kiwon Lafiyar Yara Masu Rahusa

September 14, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.