Rikicin da ya dabaibaye shugabancin hukumar kwallon kafa ta Nijeriya ya dauki wani sabon salo a ranar Talata yayinda tsoffin shugabannin Hukumar Kwallon Kafa ta Nijeriya (NFF), manyan sakatarori da masu ruwa da tsaki a kwallon kafar kasar suka gabatar da bukatunsu ga gamayyar jami’an FIFA da CAF a birnin tarayya Abuja, a yayin tattaunawar, tsoffin shugabannin NFF sun yi kira da a kafa Kwamitin da zaiyi aiki na tsawon watanni shida nan take domin gyara harkokin kwallon kafa na kasar kafin gudanar da sabon zaben shugabanni.
Taron ya kasance wani bangare na shawarwarin da FIFA da CAF ke ci gaba da yi da masu ruwa da tsaki a kwallon kafa ta Nijeriya bayan rikicin shugabanci a NFF da kuma karuwar kiraye-kirayen yin garanbawul a hukumar da dubban mutane keyi, wadanda suka halarci taron na ranar Talata sun hada da tsoffin shugabannin NFF Sani Abdullahi Lulu da Aminu Maigari, tsohon mataimakin shugaban hukumar na farko Sanata Obinna Ogba, da tsoffin sakatare-janar Sani Toro, Musa Amadu, Fanny Amun, Bolaji Ojo-Oba da Tijani Yusuf.
Haka kuma akwai shugaban Remo Stars Kunle Soname, tsohon dan wasan tawagar kwallon kafa ta Nijeriya Segun Odegbami, wakilan kungiyar Marubutan Wasanni ta Nijeriya (SWAN), karkashin jagorancin shugabanta na kasa Isaiah Benjamin da sakatare-janar Ikenna Okonkwo, da kuma tsoffin yan jarida Mitchell Obi da Mumuni Alao, a cewar Leadership Sports, tsoffin shugabannin sun gabatar da takardar hadin gwiwa da ke nuna cewa rikice-rikicen kwallon kafa da ke faruwa a Nijeriya ya samo asali ne sakamakon matsalolin gudanarwa da raunin tsarin aiki.
An cimma matsaya akan abubuwa da dama da suka hada da sake fasalik gudanarwar hukumar ta hanyar sauya tsare-tsare da dama da suka hada da bangaren kudi da walwalar yan wasa, SWAN ta jaddada cewa akwai bukatar masu sha’awar shugabantar hukumar su kansace kwararru a bangaren kwallon kafa ta Nijeriya.














