ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, July 16, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Asalin Abin Da Ya Faru Da Sheikh Sani Khalifa, Daga Bakin Ɗansa

by Sulaiman
6 months ago

Fitaccen malamin addinin Musulunci, Sheikh Sani Kalifa Zaria, bayan kwashe kwanaki fiye da 21, har yanzu iyalansa basu san inda yake ba.

 

A yayin tattaunawa da manema labarai, ɗaya daga cikin ‘ya’yansa mai suna Muhammadu Nafsu Zakiyya Sani Kalifa Zaria, ya bayyana yadda lamarin ya faru da cewa:

ADVERTISEMENT
  • Shari’ar Annabi SAW Ta Fi Ta Sauran Annabawa Sauƙi
  • A Bangaren Kyawawan Dabi’u, Annabi SAW Ma’aiki Ne Ga Duk Halitta

Akwai wani muridin (mabiyi) Sheikh Sani Kalifa wanda kuma Jami’in soja ne, ya zo wurin Sheikh da wata buƙata ta neman addu’a daga maigidansa a wurin aiki (babban jami’in soja), kan wani al’amari da suke shirin aiwatarwa Allah ya basu sa’a.

 

LABARAI MASU NASABA

Mutfwang Ya Buƙaci Sojoji Su Ƙara Ƙaimi A Aikinsu

Ba Zan Iya Jure Halayen El-Rufai Ba Shi Yasa Na Fice Daga ADC – Salihu Lukman

Nan take, sai wannan muridi ya kira ogansa a waya, ya haɗa shi da Sheikh Kalifa don su gaisa, sai wannan oga, babban jami’in soji, ya ce, “Malam ka taya mu da addu’a, akwai wani babban aiki da muke shirin aiwatarwa, Allah ya bamu sa’a.” Ba tare da ya bayyana wa Sheikh Kalifa irin abun da suke shirin aiwatarwa ba. Daga nan, sai ya nemi Kalifa ya tura asusun Banki domin sanya abun sadaƙa.

 

Bayan sun gama waya, sai wannan muridi ya karɓi nambar asusun Sheikh ya tura wa Ogansa, aka tura Naira miliyan biyu (N2,000,000) acikin asusun. Bayan kwana biyu, Sheikh Kalifa ya tura a ciro kuɗi a asusun, sai aka ce masa, an rufe asusun.

 

Da zuwan Sheikh Kalifa Bankin domin a gyara matsalar, sai aka sanar da shi cewa, matsalar daga EFCC ce kuma dole sai an je ofishinta da ke Abuja.

 

A wata ranar Alhamis, bayan sallar Asuba, Sheikh Kalifa suka shiga mota zuwa ofishin EFCC da ke Abuja, da isarsu, jami’an hukumar suka yi musu bayani cewa, wannan miliyan biyu da aka tura, itace sanadi, sai ya yi musu bayanin yadda kuɗin suka samu, sai suka ce to ya ɗan jira. Yana nan zaune, sai ga jami’an sojoji sun shigo, sai suka ce suna son za su yi wa Sheikh Kalifa bincike amma ba a nan za a yi ba, kuma binciken ba zai wuce sa’o’i uku kacal ba. Jami’an sojin, sun tafi da wani daga cikin ‘ya’yansa mai suna Ibrahim amma sun sauke shi a hanya.

 

A yayin wannan tattaunawar, an haura sati uku ba muga Sheikh Kalifa ba, sai dai ranar da ya cika sati ɗaya a wurinsu, sun bashi waya ya tuntuɓi iyalinsa. Yanzu ya zama sati biyu kenan ba a sake jin muryarsa ba.

 

Da aka fara bincike, sai aka gano cewa, wannan asusun da aka turawa Sheikh Kalifa kudi, ana zargin asusun wani babban jami’in soja ne da ake zargin yana daga cikin jami’an sojojin da suka yi yunƙurin juyin mulkin da bai yi nasara ba a watannin baya.

 

Nafsu Zakiyya, ya tabbatar da cewa, duk sun bi shugabannin Siyasa da ke Zaria, musamman kakakin majalisar wakilai, Hon. Tajudeen Abbas, Gwamnan Jihar Kaduna, Sanata Uba Sani da sarkin Zazzau, Alhaji Nuhu Bamalli domin ganin an san halin da Sheikh Kalifa ke ciki, kuma mun tabbatar dukansu suna iya bakin ƙoƙarinsu. Amma komai, za a gaya mana, in ba mun ganshi ba, hankali ba zai kwanta ba, musamman duba da shekarunsa sama da 75, riga ɗaya, takalmi ɗaya, da hula ɗaya da ya tafi da su.

Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    Tinubu Ya Miƙa Wa Shettima Takardar Tabbatar Da Shi Abokin Takararsa A Zaɓen 2027
  • Sulaiman
    Xi Jinping Ya Gana Da Shugaban Kazakhstan
  • Sulaiman
    Mutfwang Ya Buƙaci Sojoji Su Ƙara Ƙaimi A Aikinsu
  • Sulaiman
    An Yi Bikin Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Kafa Kungiyar Hadin Gwiwar Fasahar AI Ta Duniya A Shanghai

MASU ALAKA

Mutfwang Ya Buƙaci Sojoji Su Ƙara Ƙaimi A Aikinsu
Manyan Labarai

Mutfwang Ya Buƙaci Sojoji Su Ƙara Ƙaimi A Aikinsu

July 16, 2026
Gwamnatin Tarayya Na Biyan Tallafin Man Fetur A Asirce – El-Rufai
Siyasa

Ba Zan Iya Jure Halayen El-Rufai Ba Shi Yasa Na Fice Daga ADC – Salihu Lukman

July 16, 2026
M.A. Abubakar Ya Zaɓi Farouk Mustapha A Matsayin  Mataimakinsa
Manyan Labarai

M.A. Abubakar Ya Zaɓi Farouk Mustapha A Matsayin Mataimakinsa

July 16, 2026
Next Post
KSADP Ta Yi Rigakafin Dabbobi Sama da Miliyan 5.5, Ta Zuba Jari Mai Yawa a Ɓangaren Kiwo A Kano

KSADP Ta Yi Rigakafin Dabbobi Sama da Miliyan 5.5, Ta Zuba Jari Mai Yawa a Ɓangaren Kiwo A Kano

LABARAI MASU NASABA

Tinubu Ya Miƙa Wa Shettima Takardar Tabbatar Da Shi Abokin Takararsa A Zaɓen 2027

Tinubu Ya Miƙa Wa Shettima Takardar Tabbatar Da Shi Abokin Takararsa A Zaɓen 2027

July 16, 2026
Xi Jinping Ya Gana Da Shugaban Kazakhstan

Xi Jinping Ya Gana Da Shugaban Kazakhstan

July 16, 2026
Mutfwang Ya Buƙaci Sojoji Su Ƙara Ƙaimi A Aikinsu

Mutfwang Ya Buƙaci Sojoji Su Ƙara Ƙaimi A Aikinsu

July 16, 2026
An Yi Bikin Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Kafa Kungiyar Hadin Gwiwar Fasahar AI Ta Duniya A Shanghai

An Yi Bikin Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Kafa Kungiyar Hadin Gwiwar Fasahar AI Ta Duniya A Shanghai

July 16, 2026
Gwamnatin Tarayya Na Biyan Tallafin Man Fetur A Asirce – El-Rufai

Ba Zan Iya Jure Halayen El-Rufai Ba Shi Yasa Na Fice Daga ADC – Salihu Lukman

July 16, 2026
Ra’yin Sin Da Afirka Ya Zo Daya A Fannin Fasahar AI

Ra’yin Sin Da Afirka Ya Zo Daya A Fannin Fasahar AI

July 16, 2026
Duk Da Sauye-Sauyen Tattalin Arziƙi Kashi 79% Na Ƴan Nijeriya Na Cikin Talauci – Bankin Duniya

Duk Da Sauye-Sauyen Tattalin Arziƙi Kashi 79% Na Ƴan Nijeriya Na Cikin Talauci – Bankin Duniya

July 16, 2026
M.A. Abubakar Ya Zaɓi Farouk Mustapha A Matsayin  Mataimakinsa

M.A. Abubakar Ya Zaɓi Farouk Mustapha A Matsayin Mataimakinsa

July 16, 2026
Saliba Zai Yi Jinyar Watanni 5 Bayan Raunin Da Ya Samu A Bayansa

Saliba Zai Yi Jinyar Watanni 5 Bayan Raunin Da Ya Samu A Bayansa

July 16, 2026
Kotu Ta Yanke Wa Wani Hukuncin Ɗaurin Shekara 7 Kan Tallan Wiwi A Kafafen Sada Zumunta

Kotu Ta Yanke Wa Wani Hukuncin Ɗaurin Shekara 7 Kan Tallan Wiwi A Kafafen Sada Zumunta

July 16, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.