ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Asalin Abin Da Ya Faru Da Sheikh Sani Khalifa, Daga Bakin Ɗansa

by Sulaiman
6 months ago

Fitaccen malamin addinin Musulunci, Sheikh Sani Kalifa Zaria, bayan kwashe kwanaki fiye da 21, har yanzu iyalansa basu san inda yake ba.

 

A yayin tattaunawa da manema labarai, ɗaya daga cikin ‘ya’yansa mai suna Muhammadu Nafsu Zakiyya Sani Kalifa Zaria, ya bayyana yadda lamarin ya faru da cewa:

ADVERTISEMENT
  • Shari’ar Annabi SAW Ta Fi Ta Sauran Annabawa Sauƙi
  • A Bangaren Kyawawan Dabi’u, Annabi SAW Ma’aiki Ne Ga Duk Halitta

Akwai wani muridin (mabiyi) Sheikh Sani Kalifa wanda kuma Jami’in soja ne, ya zo wurin Sheikh da wata buƙata ta neman addu’a daga maigidansa a wurin aiki (babban jami’in soja), kan wani al’amari da suke shirin aiwatarwa Allah ya basu sa’a.

 

LABARAI MASU NASABA

Kotu Ta Ɗege Shari’ar Ganduje Da Wasu Mutum 7 Zuwa 14 Ga Oktoba 2026

Ndume Ya Bayyana Dalilin Da Ya Sa Yake Goyon Bayan Ƙudirin Kafa ‘Yansandan Jihohi

Nan take, sai wannan muridi ya kira ogansa a waya, ya haɗa shi da Sheikh Kalifa don su gaisa, sai wannan oga, babban jami’in soji, ya ce, “Malam ka taya mu da addu’a, akwai wani babban aiki da muke shirin aiwatarwa, Allah ya bamu sa’a.” Ba tare da ya bayyana wa Sheikh Kalifa irin abun da suke shirin aiwatarwa ba. Daga nan, sai ya nemi Kalifa ya tura asusun Banki domin sanya abun sadaƙa.

 

Bayan sun gama waya, sai wannan muridi ya karɓi nambar asusun Sheikh ya tura wa Ogansa, aka tura Naira miliyan biyu (N2,000,000) acikin asusun. Bayan kwana biyu, Sheikh Kalifa ya tura a ciro kuɗi a asusun, sai aka ce masa, an rufe asusun.

 

Da zuwan Sheikh Kalifa Bankin domin a gyara matsalar, sai aka sanar da shi cewa, matsalar daga EFCC ce kuma dole sai an je ofishinta da ke Abuja.

 

A wata ranar Alhamis, bayan sallar Asuba, Sheikh Kalifa suka shiga mota zuwa ofishin EFCC da ke Abuja, da isarsu, jami’an hukumar suka yi musu bayani cewa, wannan miliyan biyu da aka tura, itace sanadi, sai ya yi musu bayanin yadda kuɗin suka samu, sai suka ce to ya ɗan jira. Yana nan zaune, sai ga jami’an sojoji sun shigo, sai suka ce suna son za su yi wa Sheikh Kalifa bincike amma ba a nan za a yi ba, kuma binciken ba zai wuce sa’o’i uku kacal ba. Jami’an sojin, sun tafi da wani daga cikin ‘ya’yansa mai suna Ibrahim amma sun sauke shi a hanya.

 

A yayin wannan tattaunawar, an haura sati uku ba muga Sheikh Kalifa ba, sai dai ranar da ya cika sati ɗaya a wurinsu, sun bashi waya ya tuntuɓi iyalinsa. Yanzu ya zama sati biyu kenan ba a sake jin muryarsa ba.

 

Da aka fara bincike, sai aka gano cewa, wannan asusun da aka turawa Sheikh Kalifa kudi, ana zargin asusun wani babban jami’in soja ne da ake zargin yana daga cikin jami’an sojojin da suka yi yunƙurin juyin mulkin da bai yi nasara ba a watannin baya.

 

Nafsu Zakiyya, ya tabbatar da cewa, duk sun bi shugabannin Siyasa da ke Zaria, musamman kakakin majalisar wakilai, Hon. Tajudeen Abbas, Gwamnan Jihar Kaduna, Sanata Uba Sani da sarkin Zazzau, Alhaji Nuhu Bamalli domin ganin an san halin da Sheikh Kalifa ke ciki, kuma mun tabbatar dukansu suna iya bakin ƙoƙarinsu. Amma komai, za a gaya mana, in ba mun ganshi ba, hankali ba zai kwanta ba, musamman duba da shekarunsa sama da 75, riga ɗaya, takalmi ɗaya, da hula ɗaya da ya tafi da su.

Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    Wani Gidan Adana Kayan Tarihi Na Sin Ya Fitar Da Rahoton Yadda Dakarun Japan Suka Rika Zubawa Mutane Jinin Dabbobi Yayin Yakin Duniya Na Biyu
  • Sulaiman
    Wang Yi Ya Yi Kira Da A Gaggauta Bude Mashigin Hormuz
  • Sulaiman
    Ƙungiyar NPCF Ta Yi Barazanar Janye Goyon Bayanta Ga Tinubu
  • Sulaiman
    Firaministan Sin Ya Halarci Taron Tattaunawa Da Wakilan ‘Yan Kasuwa Mahalarta Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na DAVOS

MASU ALAKA

Kotu Ta Ɗege Shari’ar Ganduje Da Wasu Mutum 7 Zuwa 14 Ga Oktoba 2026
Manyan Labarai

Kotu Ta Ɗege Shari’ar Ganduje Da Wasu Mutum 7 Zuwa 14 Ga Oktoba 2026

June 25, 2026
Ndume Ya Bayyana Dalilin Da Ya Sa Yake Goyon Bayan Ƙudirin Kafa ‘Yansandan Jihohi
Manyan Labarai

Ndume Ya Bayyana Dalilin Da Ya Sa Yake Goyon Bayan Ƙudirin Kafa ‘Yansandan Jihohi

June 25, 2026
EFCC Za Ta Gurfanar Da Shugaban Miyetti Allah Kan Zargin Almundahanar Dala Miliyan 2.53
Manyan Labarai

EFCC Za Ta Gurfanar Da Shugaban Miyetti Allah Kan Zargin Almundahanar Dala Miliyan 2.53

June 25, 2026
Next Post
KSADP Ta Yi Rigakafin Dabbobi Sama da Miliyan 5.5, Ta Zuba Jari Mai Yawa a Ɓangaren Kiwo A Kano

KSADP Ta Yi Rigakafin Dabbobi Sama da Miliyan 5.5, Ta Zuba Jari Mai Yawa a Ɓangaren Kiwo A Kano

LABARAI MASU NASABA

Wani Gidan Adana Kayan Tarihi Na Sin Ya Fitar Da Rahoton Yadda Dakarun Japan Suka Rika Zubawa Mutane Jinin Dabbobi Yayin Yakin Duniya Na Biyu

Wani Gidan Adana Kayan Tarihi Na Sin Ya Fitar Da Rahoton Yadda Dakarun Japan Suka Rika Zubawa Mutane Jinin Dabbobi Yayin Yakin Duniya Na Biyu

June 25, 2026
Wang Yi Ya Yi Kira Da A Gaggauta Bude Mashigin Hormuz

Wang Yi Ya Yi Kira Da A Gaggauta Bude Mashigin Hormuz

June 25, 2026
Ƙungiyar NPCF Ta Yi Barazanar Janye Goyon Bayanta Ga Tinubu

Ƙungiyar NPCF Ta Yi Barazanar Janye Goyon Bayanta Ga Tinubu

June 25, 2026
Firaministan Sin Ya Halarci Taron Tattaunawa Da Wakilan ‘Yan Kasuwa Mahalarta Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na DAVOS

Firaministan Sin Ya Halarci Taron Tattaunawa Da Wakilan ‘Yan Kasuwa Mahalarta Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na DAVOS

June 25, 2026
Sojoji Sun Kama Mai Kai Wa Ƴan Ta’adda Kayan Aiki A Zamfara

Sojoji Sun Kama Mai Kai Wa Ƴan Ta’adda Kayan Aiki A Zamfara

June 25, 2026
Kotu Ta Ɗege Shari’ar Ganduje Da Wasu Mutum 7 Zuwa 14 Ga Oktoba 2026

Kotu Ta Ɗege Shari’ar Ganduje Da Wasu Mutum 7 Zuwa 14 Ga Oktoba 2026

June 25, 2026
An Fara Gasar Tseren Dawakai Ta ‘Renewed Hope’ da Sabon Salo A Kano

An Fara Gasar Tseren Dawakai Ta ‘Renewed Hope’ da Sabon Salo A Kano

June 25, 2026
APC Ta Dage Yakin Zaben Shugaban Kasarta A Kano

An Dakatar Da Shugaban APC Na Kebbi Da Kwamishina Kan Zaɓen Cike Gurbin Zuru

June 25, 2026
Ndume Ya Bayyana Dalilin Da Ya Sa Yake Goyon Bayan Ƙudirin Kafa ‘Yansandan Jihohi

Ndume Ya Bayyana Dalilin Da Ya Sa Yake Goyon Bayan Ƙudirin Kafa ‘Yansandan Jihohi

June 25, 2026
EFCC Za Ta Gurfanar Da Shugaban Miyetti Allah Kan Zargin Almundahanar Dala Miliyan 2.53

EFCC Za Ta Gurfanar Da Shugaban Miyetti Allah Kan Zargin Almundahanar Dala Miliyan 2.53

June 25, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.