ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Asalin Abin Da Ya Faru Da Sheikh Sani Khalifa, Daga Bakin Ɗansa

by Sulaiman
8 months ago

Fitaccen malamin addinin Musulunci, Sheikh Sani Kalifa Zaria, bayan kwashe kwanaki fiye da 21, har yanzu iyalansa basu san inda yake ba.

 

A yayin tattaunawa da manema labarai, ɗaya daga cikin ‘ya’yansa mai suna Muhammadu Nafsu Zakiyya Sani Kalifa Zaria, ya bayyana yadda lamarin ya faru da cewa:

ADVERTISEMENT
  • Shari’ar Annabi SAW Ta Fi Ta Sauran Annabawa Sauƙi
  • A Bangaren Kyawawan Dabi’u, Annabi SAW Ma’aiki Ne Ga Duk Halitta

Akwai wani muridin (mabiyi) Sheikh Sani Kalifa wanda kuma Jami’in soja ne, ya zo wurin Sheikh da wata buƙata ta neman addu’a daga maigidansa a wurin aiki (babban jami’in soja), kan wani al’amari da suke shirin aiwatarwa Allah ya basu sa’a.

 

LABARAI MASU NASABA

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

Ballon d’Or: Messi, Yamal, Da Mane Na Cikin ‘Yan Wasa 30 Da Aka Zaɓo

Nan take, sai wannan muridi ya kira ogansa a waya, ya haɗa shi da Sheikh Kalifa don su gaisa, sai wannan oga, babban jami’in soji, ya ce, “Malam ka taya mu da addu’a, akwai wani babban aiki da muke shirin aiwatarwa, Allah ya bamu sa’a.” Ba tare da ya bayyana wa Sheikh Kalifa irin abun da suke shirin aiwatarwa ba. Daga nan, sai ya nemi Kalifa ya tura asusun Banki domin sanya abun sadaƙa.

 

Bayan sun gama waya, sai wannan muridi ya karɓi nambar asusun Sheikh ya tura wa Ogansa, aka tura Naira miliyan biyu (N2,000,000) acikin asusun. Bayan kwana biyu, Sheikh Kalifa ya tura a ciro kuɗi a asusun, sai aka ce masa, an rufe asusun.

 

Da zuwan Sheikh Kalifa Bankin domin a gyara matsalar, sai aka sanar da shi cewa, matsalar daga EFCC ce kuma dole sai an je ofishinta da ke Abuja.

 

A wata ranar Alhamis, bayan sallar Asuba, Sheikh Kalifa suka shiga mota zuwa ofishin EFCC da ke Abuja, da isarsu, jami’an hukumar suka yi musu bayani cewa, wannan miliyan biyu da aka tura, itace sanadi, sai ya yi musu bayanin yadda kuɗin suka samu, sai suka ce to ya ɗan jira. Yana nan zaune, sai ga jami’an sojoji sun shigo, sai suka ce suna son za su yi wa Sheikh Kalifa bincike amma ba a nan za a yi ba, kuma binciken ba zai wuce sa’o’i uku kacal ba. Jami’an sojin, sun tafi da wani daga cikin ‘ya’yansa mai suna Ibrahim amma sun sauke shi a hanya.

 

A yayin wannan tattaunawar, an haura sati uku ba muga Sheikh Kalifa ba, sai dai ranar da ya cika sati ɗaya a wurinsu, sun bashi waya ya tuntuɓi iyalinsa. Yanzu ya zama sati biyu kenan ba a sake jin muryarsa ba.

 

Da aka fara bincike, sai aka gano cewa, wannan asusun da aka turawa Sheikh Kalifa kudi, ana zargin asusun wani babban jami’in soja ne da ake zargin yana daga cikin jami’an sojojin da suka yi yunƙurin juyin mulkin da bai yi nasara ba a watannin baya.

 

Nafsu Zakiyya, ya tabbatar da cewa, duk sun bi shugabannin Siyasa da ke Zaria, musamman kakakin majalisar wakilai, Hon. Tajudeen Abbas, Gwamnan Jihar Kaduna, Sanata Uba Sani da sarkin Zazzau, Alhaji Nuhu Bamalli domin ganin an san halin da Sheikh Kalifa ke ciki, kuma mun tabbatar dukansu suna iya bakin ƙoƙarinsu. Amma komai, za a gaya mana, in ba mun ganshi ba, hankali ba zai kwanta ba, musamman duba da shekarunsa sama da 75, riga ɗaya, takalmi ɗaya, da hula ɗaya da ya tafi da su.

Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara
  • Sulaiman
    Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5
  • Sulaiman
    Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana
  • Sulaiman
    ‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

MASU ALAKA

Sojoji
Manyan Labarai

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Ballon D'or
Manyan Labarai

Ballon d’Or: Messi, Yamal, Da Mane Na Cikin ‘Yan Wasa 30 Da Aka Zaɓo

September 8, 2026
Ɓata-gari Sun Kai Wa Ayarin Peter Obi Hari A Benue
Manyan Labarai

Ɓata-gari Sun Kai Wa Ayarin Peter Obi Hari A Benue

September 8, 2026
Next Post
KSADP Ta Yi Rigakafin Dabbobi Sama da Miliyan 5.5, Ta Zuba Jari Mai Yawa a Ɓangaren Kiwo A Kano

KSADP Ta Yi Rigakafin Dabbobi Sama da Miliyan 5.5, Ta Zuba Jari Mai Yawa a Ɓangaren Kiwo A Kano

LABARAI MASU NASABA

Sojoji

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.