Majalisar Dattawan Nijeriya ta amince da bayar da tallafin Naira miliyan 50 ga iyalan malamai biyu da aka kashe yayin da suke hannun masu garkuwa da mutane, da kuma jami’an tsaro uku da suka rasa rayukansu yayin aikin ceto ɗalibai 39 da malamai bakwai da aka yi garkuwa da su daga al’ummomin Ahoro-Esinle, Yawota da Alawusa a ranar 15 ga Mayun 2026.
A ranar 10 ga Yuli, Fadar Shugaban Ƙasa ta sanar da cewa an yi nasarar ceto dukkan ɗaliban da malamansu da aka sace a Ƙaramar Hukumar Oriire ta Jihar Oyo. Haka kuma, jami’an tsaro sun kama mutane takwas da ake zargin masu garkuwa da mutane ne, yayin da aka kashe wasu a lokacin aikin ceton.
Mai Ba Shugaban Ƙasa Shawara na Musamman kan Yaɗa Labarai da Dabaru, Bayo Onanuga, ne ya bayyana hakan a wani saƙo da ya wallafa a shafinsa na X.
Shugaban Majalisar Dattawa, Godswill Akpabio, ya sanar da bayar da tallafin a zaman majalisar na ranar Laraba, inda ya bayyana cewa wannan kyauta alama ce ta girmamawa da godiya ga sadaukarwar da malaman da jami’an tsaron da suka mutu suka yi.
Akpabio ya kuma yabawa shugabannin hukumomin tsaro, ciki har da Babban Hafsan Sojin Ƙasa, Darakta Janar na DSS, Sufeto Janar na ’Yansanda, Ministan Tsaro da kuma Bola Ahmed Tinubu, bisa rawar da suka taka wajen gudanar da aikin ceton














