‘Yan bindiga sun sace shugaban makarantar sakandaren gwamnati da ke Odo-Ekina tare da wani jami’in Hukumar Shirya Jarabawar NECO da ɗalibai huɗu yayin gudanar da jarabawar NECO a Karamar Hukumar Dekina ta Jihar Kogi.
Lamarin ya faru ne da yammacin ranar Talata yayin da ɗaliban ke rubuta jarabawa.
Rundunar ‘yansandan jihar ta ce maharan sun kutsa cikin makarantar tare da yin awon gaba da waɗanda abin ya shafa.
Kakakin Rundunar ‘Yansandan Jihar Kogi, SP Salisu Oyiza, ta ce jami’an tsaro sun fara aikin ceto waɗanda aka sace.
Ta ce an ceto ɗaya daga cikin ɗaliban da aka sace, yayin da ake ci gaba da ƙoƙarin ceto sauran.
Kwamishinan ‘Yansandan jihar tare da sauran jami’an tsaro sun kai ziyara yankin domin tantance halin da ake ciki.
Rundunar ta ce za ta yi ƙarin bayani bayan kammala bincike.
Lamarin ya sake haifar da fargaba kan hare-haren da ake kai wa makarantu a Jihar Kogi.
Jami’an tsaro sun ce suna ci gaba da ƙoƙarin ceto sauran waɗanda aka sace tare da kamo waɗanda suka kai harin.













