Shugaban ƙasar Turkiyya, Recep Tayyip Erdoğan, ya bayyana cewa irin jajircewar da al’ummar ƙasarsa suka nuna wajen dakile yunƙurin juyin mulki na ranar 15 ga Yulin 2016 ita ce mafi girman misalin kare dimokuraɗiyya a tarihin duniya.
A cikin saƙon da ya fitar domin tunawa da cika shekaru goma da yunƙurin juyin mulkin da bai yi nasara ba, Erdoğan ya ce ranar 15 ga Yuli ta kasance ɗaya daga cikin ranakun da suka fi muni a tarihin siyasar Turkiyya, amma kuma ta zama wata rana da ta nuna ƙarfi da jajircewar al’umma wajen kare dimokuraɗiyya.
Ya zargi ƙungiyar ‘yan ta’adda ta Fetullahist Terrorist Organisation (FETO) da shirya yunƙurin juyin mulkin, yana mai cewa manufarsu ita ce jefa ƙasar cikin rikici na dogon lokaci tare da tauye ikon mallakar ƙasar.
Erdoğan ya ce: “Ta hanyar tsayawa tsayin daka domin kare ‘yancinsu da makomarsu tare da fuskantar masu juyin mulki, al’ummar Turkiyya sun nuna wa duniya cewa muradin jama’a ba zai taɓa rushewa a wannan ƙasa ba,”
“Hikima, jarumtaka da hangen nesan da al’ummar Turkiyya suka nuna a daren 15 ga Yuli ba su da tamka a tarihin dimokuraɗiyyar duniya.” A cewar Erdoğan.
Shugaban ya bayyana cewa yunƙurin juyin mulkin bai kasance kawai wani yunƙuri na sojoji na ƙwace mulki ba, illa ya kasance wani hari da aka kai kan ‘yancin kai da cikakken ikon Turkiyya. Ya ce Fadar Shugaban Ƙasa da Majalisar Dokokin Turkiyya na daga cikin manyan wuraren da aka yi niyyar kai wa hari, saboda suna wakiltar ikon jama’a da dimokuraɗiyya.
Erdoğan ya tuna da jawabin da ya yi wa al’umma a daren juyin mulkin, inda ya jaddada cewa babu wata hukuma da ya fi girmamawa kamar ikon jama’a.
Ya ce ya yi wannan furuci ne cikin cikakken tabbacin cewa al’ummar Turkiyya za su tsaya tsayin daka wajen kare muradinsu da tsarin dimokuraɗiyya.
A ƙarshe, shugaban ya yaba wa ‘yan ƙasar da suka fito kan tituna cikin ƙarfin hali da azama domin fuskantar masu juyin mulki, duk da haɗarin rasa rayukansu, yana mai cewa wannan ya tabbatar da ƙudurin al’ummar Turkiyya na kare dimokuraɗiyya da ’yancin ƙasarsu.














