Tsohon ɗan takarar gwamna na jam’iyyar Social Democratic Party (SDP) a zaɓen 2023 a Jihar Gombe, Kelmi Jeacob Lazarus, ya koma jam’iyyar PDP.
Kelmi, ya sanar da sauya sheƙarsa a ranar Talata, inda ya bayyana cewa ya ɗauki matakin ne bayan tuntuɓar magoya bayansa a fa6din jihar.
Ya kuma bayyana goyon bayansa ga Farfesa Isa Ali Pantami gabanin zaɓen gwamna na 2027, yana mai cewa Pantami na da ƙwarewa, hangen nesa da nagartar jagoranci da za su ciyar da Jihar Gombe gaba.
Kelmi ya buƙaci magoya bayansa da al’ummar jihar su haɗa kai da jam’iyyar PDP domin tabbatar da nasararta a zaɓen gwamna mai zuwa.
Mambobin PDP a jihar sun yi maraba da shigowar Kelmi cikin jam’iyyar, inda suka ce sauya sheƙarsa zai ƙara wa PDP ƙarfi kafin zaɓen 2027.
Sun bayyana cewar shigowarsa cikin jam’iyyar zai taimaka wajen ƙara wa PDP magoya baya yayin da ake shirye-shiryen tunkarar zaɓen 2027.













