Babban Kwamandan Hukumar Hisbah ta Jihar Kano, Sheikh Aminu Ibrahim Daurawa, ya gargadi ma’auratan da za su shiga shirin auren gata na jihar cewa babu saki ba tare da sahalewar hukumar Hisbah ba.
Daurawa ya bayyana hakan ne yayin wata ziyara da ya kai hedikwatar Hukumar Yaki da Cutar Kanjamau ta Jihar Kano (KSACA), daya daga cikin wuraren da ake gudanar da gwaje-gwajen lafiya ga masu shirin yin auren.Ya ce gwamnatin jihar na kashe makudan kudade wajen gudanar da shirin, don haka tana sa ran auren zai kasance mai dorewa.
A cewarsa, “Ba ma son saki. Duk wanda yake son ya saki matarsa ko ta nemi rabuwa da mijinta saboda wani dalili, dole ne ya zo Hisbah tunda a nan aka daura auren. Muna da kwamitin sulhu wanda zai zauna ya sasanta matsalolin da ke tsakanin ma’auratan kafin a yi la’akari da rabuwa.”
Daurawa ya kara da cewa manufar hakan ita ce karfafa zaman lafiya a tsakanin ma’aurata da kuma rage yawan mace-macen aure a cikin al’umma.














Discussion about this post