Kasuwa Ce Ke Saita Tsarin Cinikayyar Sin Da EU In Ji Kakakin Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin
Mai magana da yawun ma’aikatar harkokin wajen kasar Sin Mao Ning, ta ce abu ne a fili cewa kayayyaki da...
Mai magana da yawun ma’aikatar harkokin wajen kasar Sin Mao Ning, ta ce abu ne a fili cewa kayayyaki da...
Bayan shafe tsawon shekaru 105 da kafuwar Jam’iyyar Kwaminis ta Kasar Sin da yadda gwamnati karkashin jam’iyyar ke ci gaba da jagorantar kasar Sin cikin hikima da hangen nesa da tarin nasarori, ba na zaton akwai wani abu da gwamnati za ta bullo da shi, da zai sa a ga baikenta kamar yadda wasu suke yi. Salon shugabanci da nasarorin da kasar Sin ta samu cikin gomman shekaru, ya nuna mana cewa, gwamnatin kasa ce kadai ke da alhakin tafiyar da harkokinta yadda ya dace da yanayi da jama’arta, kuma ita ce ta fi kowa sanin abun da ya dace da al’ummarta. Yadda wasu kasashen yamma da kafafensu na yada labarai ke kokarin jirkitawa da yada jita-jita game da sabuwar dokar kasar Sin dake nufin kara tabbatar da dunkule dukkan kabilun kasar wuri guda, abun mamaki ne matuka. Manufar dokar dai ita ce karfafa hadin kan kasa da tabbatar da daidaito da kuma inganta mu’amala tsakanin kabilu daban-daban. Duk wanda ke bibiya ko ya ziyarta ko yake zaune a kasar Sin kamar ni, to tabbas ya san yadda gwamnatin kasar ke mayar da hankali kan dukkan al’ummominta ba tare da wariya ko son kai ba, don haka me ya sa za ta fitar da dokar da za ta nuna wariya ko musgunawa jama’arta? Daya daga cikin abubuwan da suka haifar da hadin kai da ci gaban al’ummar kasar Sin shi ne, sanin cewa dukkansu Sinawa, ’yan uwan juna, kuma tsintsiya madaurinki daya, kishin kasarsu na gaba da komai. Kuma wannan kishin da suke da shi a zukatansu ne, kashin bayan ci gaban da suke samu a kai a kai kuma na ban mamaki. A tunanina, masu fassara wannan doka ta bahaguwar hanya, na yi ne domin cimma wata manufa tasu, ko kuma son ganin al’ummomin kasar sun fada cikin matsalar rarrabuwar kawuna kamar yadda suke ciki, abun da na yi imanin kasar Sin ba za ta taba bari ba. (Fa’iza Mustapha)
Aƙalla mutane 15 ne suka rasu a wani mummunan hatsarin mota da ya afku a yankin Makabartar Musulmi da ke...
Gwamnatin Sin ta aika da zagayen farko na kayayyakin agajin gaggawa ga Venezuela, domin tallafa wa ayyukan jin kai sanadiyyar...
Hukumar kwallon ta nahiyar Turai (UEFA) ta soki matakin da hukumar kwallon kasa ta Duniya (FIFA) ta dauka na dakatar...
shugabannin Sin da Madagascar sun yi musayar sakon taya murnar cika shekaru 20da kulla alakar diflomasiyya tsakaninsu A yau 6 ga watan Yuli, shugaban kasar Sin Xi Jinping ya yi musayar sakon taya murna da shugaban Montenegro Jakov Milatović, don murnar cika shekaru 20 da kulla alakar diflomasiyya tsakanin kasashen biyu. Bangarorin biyu suna fatan yin amfani da wannan zarafi mai kyau don zurfafa hadin gwiwa mai amfani ga juna, da samar da kyakkyawar rayuwa ga al'ummomin kasashen biyu, da kuma bayar da gudunmawa ga inganta zaman lafiya da ci gaban duniya. (Amina Xu)
Dan Majalisar Wakilai mai wakiltar mazaɓar Pankshin/Kanke/Kanam a Tarayya, Yusuf Gagdi, ya nuna adawarsa ga shirin gyaran hali na ’yan...
A yayin taron kwamitin kare hakkin dan Adam na MDD(UNHRC) karo na 62, asusun bunkasa hakkin dan Adam na kasar Sin ya shirya wani taron gefe. A gun taron, wani masanin Sin ya yi maganar da ta burge kowa, inda ya ce, "Ma'auni na gaske dake tantance yanayin hakkin dan Adam na wata kasa, ba wani tsari ba ne, sai dai ko al’ummar wannan kasa suna rayuwa da mutunci da tabbaci da kuma ci gaba." Bisa nazarin da aka yi, na ce, tun daga shekara ta 2009, Sin ta tsara da aiwatar da shirye-shiryen raya ayyukan hakkin dan Adam na kasa, wanda hakan ba wai kawai ya nuna alkawarin da ta yi wa al'ummarta da duniya ba, har ma ya samar da abin koyi ga kasa da kasa kan jagorantar harkokin hakkin dan Adam. Alkaluma sun nuna cewa, a shekara ta 2025, jimillar GDP na Sin ya kai sama da Yuan tiriliyan 140, kuma matsakaicin kudin shiga na kowane mutum a ko wace shekara ya kai Yuan 43,377, wanda ya karu da kashi 5.0%, idan aka kwatanta da shekarar da ta gabace ta. Adadin wadanda suka shiga inshorar ritaya mai tushe ya kai mutane biliyan 1.076, adadin da ya kiyaye matsayin kashi 95%. Karin guraben aikin yi da aka samar a wannan shekara ya kai miliyan 12.67. Yawan masu shiga karatun tilas na tsawon shekaru 9 na kasar ya kuma kiyaye kashi 96.1%, kuma adadin daliban da ke karatu a jami’o’i ko kwalejoji ya wuce miliyan 43. Wadannan alkaluma sun shaida nasarorin da kasar ta samu a kokarinta na tabbatar da hakkin al’ummarta, kuma suna nuna yadda take aiwatar da manufar "sanya muradun jama’a a gaban komai" da kuma kare "’yancin rayuwar Sinawa". A yankin Xizang na kasar Sin, a da yawan mutanen da ke fama da jahilci ya kai sama da kashi 95%, amma yanzu an gina cikakken tsarin samar da ilimi na zamani, kuma ana aiwatar da manufar ba da ilimin kyauta na shekaru 15, wanda ya shafi daga matakin gidan renon yara zuwa sakandare. Tsawon rayuwar mutane a yankin ya kuma karu daga shekaru 35.5 a shekarar 1951 zuwa shekaru 72.19 a yanzu. A yankin Xinjiang na Sin, gwamnatin yankin ta kokarin bunkasa masana'antar noma, kamar noman auduga da kuma noman 'ya'yan itatuwa na musamman, don inganta amfani da filayen karkara da kuma kara kudin shigar manoma. A wasu yankuna, an gina makarantun koyon sana'o'i, inda ake ba da horo na musamman kamar aikin lantarki, aikin gida, da kasuwanci ta yanar gizo, don bai wa manoma da makiyaya damar koyon ilmin masana'antu. Wadannan alkaluma da al’amura na bayyana yadda kasar Sin ke kokarin tabbatar da hakkin dan Adam. Tun bayan kafuwar kwamitin kare hakkin dan Adam na MDD shekaru 20 da suka gabata, har yanzu akwai sauran rina a kaba wajen kula da hakkin dan Adam na duniya. Ayyukan kare hakkin dan Adam na Sin sun ba da mafita madaidaiciya, wato hakkin dan Adam ba hujjar sukar sauran kasashe ba ne, a'a, dabara ce ta samun ci gaba, wato misali girbin gona da kudin shigar jama'a da karatun yara a makarantu, kana da ayyukan yi masu dorewa da ingantuwar rayuwar al’umma. Misalin da Sin take bayarwa dangane da rayuwa da muradun jama’a, ya zama mai ma’ana wajen murnar cika shekaru 20 da kafuwar kwamitin. Wannan kuma ita ce mafi kyawun matakin dake bayyana "Hakkin dan Adam na dukkan bil'adama". (Marubuciya: MINA)
ADC Ta Rushe Shugabannin Jam’iyyar a Kano, Ta Naɗa Kwamitin RiƙoJam’iyyar ADC ta rushe kwamitin gudanarwa na jam’iyyar a Jihar...
Rundunar sojin ruwa ta kasar Sin, ta ce wani jirgin ruwanta mai nutso mai makaman nukiliya, ya yi nasarar harba...
© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.
© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.