ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Monday, July 27, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Mu Leka Yadda Kasar Sin Ke Raya Hakkin Dan Adam Daga Taron Gefe Na UNHRC

by Sulaiman and CGTN Hausa
3 weeks ago
UNHRC

A yayin taron kwamitin kare hakkin dan Adam na MDD(UNHRC) karo na 62, asusun bunkasa hakkin dan Adam na kasar Sin ya shirya wani taron gefe. A gun taron, wani masanin Sin ya yi maganar da ta burge kowa, inda ya ce, “Ma’auni na gaske dake tantance yanayin hakkin dan Adam na wata kasa, ba wani tsari ba ne, sai dai ko al’ummar wannan kasa suna rayuwa da mutunci da tabbaci da kuma ci gaba.”  

Bisa nazarin da aka yi, na ce, tun daga shekara ta 2009, Sin ta tsara da aiwatar da shirye-shiryen raya ayyukan hakkin dan Adam na kasa, wanda hakan ba wai kawai ya nuna alkawarin da ta yi wa al’ummarta da duniya ba, har ma ya samar da abin koyi ga kasa da kasa kan jagorantar harkokin hakkin dan Adam.  

Alkaluma sun nuna cewa, a shekara ta 2025, jimillar GDP na Sin ya kai sama da Yuan tiriliyan 140, kuma matsakaicin kudin shiga na kowane mutum a ko wace shekara ya kai Yuan 43,377, wanda ya karu da kashi 5.0%, idan aka kwatanta da shekarar da ta gabace ta. Adadin wadanda suka shiga inshorar ritaya mai tushe ya kai mutane biliyan 1.076, adadin da ya kiyaye matsayin kashi 95%. Karin guraben aikin yi da aka samar a wannan shekara ya kai miliyan 12.67. Yawan masu shiga karatun tilas na tsawon shekaru 9 na kasar ya kuma kiyaye kashi 96.1%, kuma adadin daliban da ke karatu a jami’o’i ko kwalejoji ya wuce miliyan 43. Wadannan alkaluma sun shaida nasarorin da kasar ta samu a kokarinta na tabbatar da hakkin al’ummarta, kuma suna nuna yadda take aiwatar da manufar “sanya muradun jama’a a gaban komai” da kuma kare “’yancin rayuwar Sinawa”. 

ADVERTISEMENT

A yankin Xizang na kasar Sin, a da yawan mutanen da ke fama da jahilci ya kai sama da kashi 95%, amma yanzu an gina cikakken tsarin samar da ilimi na zamani, kuma ana aiwatar da manufar ba da ilimin kyauta na shekaru 15, wanda ya shafi daga matakin gidan renon yara zuwa sakandare. Tsawon rayuwar mutane a yankin ya kuma karu daga shekaru 35.5 a shekarar 1951 zuwa shekaru 72.19 a yanzu. A yankin Xinjiang na Sin, gwamnatin yankin ta kokarin bunkasa masana’antar noma, kamar noman auduga da kuma noman ‘ya’yan itatuwa na musamman, don inganta amfani da filayen karkara da kuma kara kudin shigar manoma. A wasu yankuna, an gina makarantun koyon sana’o’i, inda ake ba da horo na musamman kamar aikin lantarki, aikin gida, da kasuwanci ta yanar gizo, don bai wa manoma da makiyaya damar koyon ilmin masana’antu. Wadannan alkaluma da al’amura na bayyana yadda kasar Sin ke kokarin tabbatar da hakkin dan Adam. 

Tun bayan kafuwar kwamitin kare hakkin dan Adam na MDD shekaru 20 da suka gabata, har yanzu akwai sauran rina a kaba wajen kula da hakkin dan Adam na duniya. Ayyukan kare hakkin dan Adam na Sin sun ba da mafita madaidaiciya, wato hakkin dan Adam ba hujjar sukar sauran kasashe ba ne, a’a, dabara ce ta samun ci gaba, wato misali girbin gona da kudin shigar jama’a da karatun yara a makarantu, kana da ayyukan yi masu dorewa da ingantuwar rayuwar al’umma. Misalin da Sin take bayarwa dangane da rayuwa da muradun jama’a, ya zama mai ma’ana wajen murnar cika shekaru 20 da kafuwar kwamitin. Wannan kuma ita ce mafi kyawun matakin dake bayyana “Hakkin dan Adam na dukkan bil’adama”. (Marubuciya: MINA) 

LABARAI MASU NASABA

Yadda Kasar Sin Ta Samar Da Ci Gaba Na Bai Daya

Sin Tana Son More Damammakin Fasahar AI a Maimakon Babakere a Wannan Bangare Da Kasashen Yamma Suka Dade Suna Yi

UNHRC
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Saura Kwanaki 100 A Bude CIIE Karo Na 9
  • Sulaiman
    Ribar Manyan Kamfanonin Sarrafa Kayayyaki Na Sin Ta Karu Da Kaso 18.7 A Rabin Farkon Bana
  • Sulaiman
    Xi: Sin Ta Shirya Kara Karfafa Dangantaka Da Brazil
  • Sulaiman
    Tinubu Ya Goyi Bayan Kafa Sabon Asibitin Koyarwa A Bichi — Ɗan Majalisar Kano
UNHRC
CGTN Hausa
+ posts Bio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Saura Kwanaki 100 A Bude CIIE Karo Na 9
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Ribar Manyan Kamfanonin Sarrafa Kayayyaki Na Sin Ta Karu Da Kaso 18.7 A Rabin Farkon Bana
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Xi: Sin Ta Shirya Kara Karfafa Dangantaka Da Brazil
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Sin Za Ta Ci Gaba Da Kare Ikon Mulkin Yankuna Da Hakkoki Da Moriyarta Ta Teku

MASU ALAKA

Yadda Kasar Sin Ta Samar Da Ci Gaba Na Bai Daya
Ra'ayi Riga

Yadda Kasar Sin Ta Samar Da Ci Gaba Na Bai Daya

July 24, 2026
Sin Tana Son More Damammakin Fasahar AI a Maimakon Babakere a Wannan Bangare Da Kasashen Yamma Suka Dade Suna Yi
Ra'ayi Riga

Sin Tana Son More Damammakin Fasahar AI a Maimakon Babakere a Wannan Bangare Da Kasashen Yamma Suka Dade Suna Yi

July 24, 2026
Me Ya Sa Ra’ayin Duniya Ke Karkata Zuwa Sin Yayin da Tasirin Amurka Ke Faduwa?
Ra'ayi Riga

Me Ya Sa Ra’ayin Duniya Ke Karkata Zuwa Sin Yayin da Tasirin Amurka Ke Faduwa?

July 23, 2026
Next Post
Rashin Tsaro: Kisa Ne Ya Fi Cancanta Ga ‘Yan Ta’adda Ba Gyaran Hali Ba – Ɗan Majalisa Gagdi

Rashin Tsaro: Kisa Ne Ya Fi Cancanta Ga 'Yan Ta'adda Ba Gyaran Hali Ba - Ɗan Majalisa Gagdi

LABARAI MASU NASABA

Saura Kwanaki 100 A Bude CIIE Karo Na 9

Saura Kwanaki 100 A Bude CIIE Karo Na 9

July 27, 2026
UNHRC

Obi-Kwankwaso Obasanjo Yake Goyon Baya, Amma Atiku Zai Iya Lashe Zabe – Momodu

July 27, 2026
Ribar Manyan Kamfanonin Sarrafa Kayayyaki Na Sin Ta Karu Da Kaso 18.7 A Rabin Farkon Bana

Ribar Manyan Kamfanonin Sarrafa Kayayyaki Na Sin Ta Karu Da Kaso 18.7 A Rabin Farkon Bana

July 27, 2026
Xi: Sin Ta Shirya Kara Karfafa Dangantaka Da Brazil

Xi: Sin Ta Shirya Kara Karfafa Dangantaka Da Brazil

July 27, 2026
Tinubu Ya Goyi Bayan Kafa Sabon Asibitin Koyarwa A Bichi — Ɗan Majalisar Kano

Tinubu Ya Goyi Bayan Kafa Sabon Asibitin Koyarwa A Bichi — Ɗan Majalisar Kano

July 27, 2026
‘Yan Bindiga Sun Kashe Mutane 30, Sun Ƙone Gidaje Da Shaguna A Kaduna 

‘Yan Bindiga Sun Kashe Mutane 30, Sun Ƙone Gidaje Da Shaguna A Kaduna 

July 27, 2026
Kwalejin Kimiyya Ta Kogi Ta Dakatar Da Malamai Kan Zargin Lalata Da Ɗalibai Da Sauran Laifuka

Kwalejin Kimiyya Ta Kogi Ta Dakatar Da Malamai Kan Zargin Lalata Da Ɗalibai Da Sauran Laifuka

July 27, 2026
Rashin Tsaro Na Barazana Ga Zaben 2027 —Rahotanni

Kuri’u Za Su Yi Tasiri A Zaɓen 2027, In Ji INEC

July 27, 2026
Auto Draft

ADC Ta Buƙaci Tinubu Ya Bai Wa Waɗanda Aka Sace A Kaiama Da Borno Kulawa

July 27, 2026
UNHRC

Sojojin Ruwa Sun Cafke Jirgin Ruwa Maƙare Da Ɗanyen Mai Na Sata

July 26, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.