ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Monday, July 6, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Mu Leka Yadda Kasar Sin Ke Raya Hakkin Dan Adam Daga Taron Gefe Na UNHRC

by Sulaiman and CGTN Hausa
56 minutes ago
UNHRC

A yayin taron kwamitin kare hakkin dan Adam na MDD(UNHRC) karo na 62, asusun bunkasa hakkin dan Adam na kasar Sin ya shirya wani taron gefe. A gun taron, wani masanin Sin ya yi maganar da ta burge kowa, inda ya ce, “Ma’auni na gaske dake tantance yanayin hakkin dan Adam na wata kasa, ba wani tsari ba ne, sai dai ko al’ummar wannan kasa suna rayuwa da mutunci da tabbaci da kuma ci gaba.”  

Bisa nazarin da aka yi, na ce, tun daga shekara ta 2009, Sin ta tsara da aiwatar da shirye-shiryen raya ayyukan hakkin dan Adam na kasa, wanda hakan ba wai kawai ya nuna alkawarin da ta yi wa al’ummarta da duniya ba, har ma ya samar da abin koyi ga kasa da kasa kan jagorantar harkokin hakkin dan Adam.  

Alkaluma sun nuna cewa, a shekara ta 2025, jimillar GDP na Sin ya kai sama da Yuan tiriliyan 140, kuma matsakaicin kudin shiga na kowane mutum a ko wace shekara ya kai Yuan 43,377, wanda ya karu da kashi 5.0%, idan aka kwatanta da shekarar da ta gabace ta. Adadin wadanda suka shiga inshorar ritaya mai tushe ya kai mutane biliyan 1.076, adadin da ya kiyaye matsayin kashi 95%. Karin guraben aikin yi da aka samar a wannan shekara ya kai miliyan 12.67. Yawan masu shiga karatun tilas na tsawon shekaru 9 na kasar ya kuma kiyaye kashi 96.1%, kuma adadin daliban da ke karatu a jami’o’i ko kwalejoji ya wuce miliyan 43. Wadannan alkaluma sun shaida nasarorin da kasar ta samu a kokarinta na tabbatar da hakkin al’ummarta, kuma suna nuna yadda take aiwatar da manufar “sanya muradun jama’a a gaban komai” da kuma kare “’yancin rayuwar Sinawa”. 

ADVERTISEMENT

A yankin Xizang na kasar Sin, a da yawan mutanen da ke fama da jahilci ya kai sama da kashi 95%, amma yanzu an gina cikakken tsarin samar da ilimi na zamani, kuma ana aiwatar da manufar ba da ilimin kyauta na shekaru 15, wanda ya shafi daga matakin gidan renon yara zuwa sakandare. Tsawon rayuwar mutane a yankin ya kuma karu daga shekaru 35.5 a shekarar 1951 zuwa shekaru 72.19 a yanzu. A yankin Xinjiang na Sin, gwamnatin yankin ta kokarin bunkasa masana’antar noma, kamar noman auduga da kuma noman ‘ya’yan itatuwa na musamman, don inganta amfani da filayen karkara da kuma kara kudin shigar manoma. A wasu yankuna, an gina makarantun koyon sana’o’i, inda ake ba da horo na musamman kamar aikin lantarki, aikin gida, da kasuwanci ta yanar gizo, don bai wa manoma da makiyaya damar koyon ilmin masana’antu. Wadannan alkaluma da al’amura na bayyana yadda kasar Sin ke kokarin tabbatar da hakkin dan Adam. 

Tun bayan kafuwar kwamitin kare hakkin dan Adam na MDD shekaru 20 da suka gabata, har yanzu akwai sauran rina a kaba wajen kula da hakkin dan Adam na duniya. Ayyukan kare hakkin dan Adam na Sin sun ba da mafita madaidaiciya, wato hakkin dan Adam ba hujjar sukar sauran kasashe ba ne, a’a, dabara ce ta samun ci gaba, wato misali girbin gona da kudin shigar jama’a da karatun yara a makarantu, kana da ayyukan yi masu dorewa da ingantuwar rayuwar al’umma. Misalin da Sin take bayarwa dangane da rayuwa da muradun jama’a, ya zama mai ma’ana wajen murnar cika shekaru 20 da kafuwar kwamitin. Wannan kuma ita ce mafi kyawun matakin dake bayyana “Hakkin dan Adam na dukkan bil’adama”. (Marubuciya: MINA) 

LABARAI MASU NASABA

Ga “Itacen Kuka” Na Kasar Sin

Shekaru 105 Na Jam’iyyar Kwaminis Ta Kasar Sin: Darussa Ga Kasashe Masu Tasowa Daga Kwarewar Ci Gaban Kasar Sin

UNHRC
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Rashin Tsaro: Kisa Ne Ya Fi Cancanta Ga ‘Yan Ta’adda Ba Gyaran Hali Ba – Ɗan Majalisa Gagdi
  • Sulaiman
    ADC Ta Rushe Shugabannin Jam’iyyar A Kano, Ta Naɗa Kwamitin Riƙo
  • Sulaiman
    Rundunar Sojin Ruwan Sin Ta Yi Gwajin Makami Mai Linzami Ta Amfani Da Jirgin Ruwa Mai Nutso
  • Sulaiman
    Kwankwaso Ya Yi Ta’aziyyar ’Ya’yan Tsohon Mataimakin Gwamnan Bauchi da Suka Rasu a Hatsarin Mota
UNHRC
CGTN Hausa
+ posts Bio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Rundunar Sojin Ruwan Sin Ta Yi Gwajin Makami Mai Linzami Ta Amfani Da Jirgin Ruwa Mai Nutso
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    An Kaddamar Da Atisayen Hadin Gwiwa Mai Taken “Hadin Gwiwar Ayyuka Kan Teku-2026” Tsakanin Sin Da Rasha
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Sabbin Shaidu Sun Bulla Dake Kara Tabbatar Da Ta’asar Amfani Da Sinadarai Masu Guba Yayin Da Dakarun Japan Ke Mamaya A Sassan Kasar Sin
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    An Gabatar Da Littafin “Bayanan Xi Jinping Kan Basirar Gudanar Da Ayyuka A Kananan Hukumomi”

MASU ALAKA

Ga “Itacen Kuka” Na Kasar Sin
Ra'ayi Riga

Ga “Itacen Kuka” Na Kasar Sin

July 1, 2026
Shekaru 105 Na Jam’iyyar Kwaminis Ta Kasar Sin: Darussa Ga Kasashe Masu Tasowa Daga Kwarewar Ci Gaban Kasar Sin
Ra'ayi Riga

Shekaru 105 Na Jam’iyyar Kwaminis Ta Kasar Sin: Darussa Ga Kasashe Masu Tasowa Daga Kwarewar Ci Gaban Kasar Sin

June 30, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”
Ra'ayi Riga

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Next Post
Rashin Tsaro: Kisa Ne Ya Fi Cancanta Ga ‘Yan Ta’adda Ba Gyaran Hali Ba – Ɗan Majalisa Gagdi

Rashin Tsaro: Kisa Ne Ya Fi Cancanta Ga 'Yan Ta'adda Ba Gyaran Hali Ba - Ɗan Majalisa Gagdi

LABARAI MASU NASABA

Rashin Tsaro: Kisa Ne Ya Fi Cancanta Ga ‘Yan Ta’adda Ba Gyaran Hali Ba – Ɗan Majalisa Gagdi

Rashin Tsaro: Kisa Ne Ya Fi Cancanta Ga ‘Yan Ta’adda Ba Gyaran Hali Ba – Ɗan Majalisa Gagdi

July 6, 2026
Mu Leka Yadda Kasar Sin Ke Raya Hakkin Dan Adam Daga Taron Gefe Na UNHRC

Mu Leka Yadda Kasar Sin Ke Raya Hakkin Dan Adam Daga Taron Gefe Na UNHRC

July 6, 2026
ADC Ta Rushe Shugabannin Jam’iyyar A Kano, Ta Naɗa Kwamitin Riƙo

ADC Ta Rushe Shugabannin Jam’iyyar A Kano, Ta Naɗa Kwamitin Riƙo

July 6, 2026
Rundunar Sojin Ruwan Sin Ta Yi Gwajin Makami Mai Linzami Ta Amfani Da Jirgin Ruwa Mai Nutso

Rundunar Sojin Ruwan Sin Ta Yi Gwajin Makami Mai Linzami Ta Amfani Da Jirgin Ruwa Mai Nutso

July 6, 2026
Yadda Na Sayar Da Kadarori Na Don Ɗaukar Nauyin Ɗalibai A Ƙasashen Waje – Kwankwaso

Kwankwaso Ya Yi Ta’aziyyar ’Ya’yan Tsohon Mataimakin Gwamnan Bauchi da Suka Rasu a Hatsarin Mota

July 6, 2026
An Kaddamar Da Atisayen Hadin Gwiwa Mai Taken “Hadin Gwiwar Ayyuka Kan Teku-2026” Tsakanin Sin Da Rasha

An Kaddamar Da Atisayen Hadin Gwiwa Mai Taken “Hadin Gwiwar Ayyuka Kan Teku-2026” Tsakanin Sin Da Rasha

July 6, 2026
Mutane 15 Sun Mutu A Wani Mummunan Hatsarin Mota, 17 Sun Jikkata

Mutane 15 Sun Mutu A Wani Mummunan Hatsarin Mota, 17 Sun Jikkata

July 6, 2026
Hukuncin Kisa Ne Ya Dace Da Ƴan Ta’adda Ba Gyaran Hali Ba – Gagdi

Hukuncin Kisa Ne Ya Dace Da Ƴan Ta’adda Ba Gyaran Hali Ba – Gagdi

July 6, 2026
Kotu Ta Ɗage Shari’ar Kwace Kadarori 57 Na Tsohon Minista Malami

Kotu Ta Ɗage Shari’ar Kwace Kadarori 57 Na Tsohon Minista Malami

July 6, 2026
Ƴan Bindiga Sun Kashe Manoma 9, Sun Sace Da Dama A Birnin Gwari

Ƴan Bindiga Sun Kashe Manoma 9, Sun Sace Da Dama A Birnin Gwari

July 6, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.