Dan Majalisar Wakilai mai wakiltar mazaɓar Pankshin/Kanke/Kanam a Tarayya, Yusuf Gagdi, ya nuna adawarsa ga shirin gyaran hali na ’yan ta’adda da sauran masu aikata manyan laifukan tashin hankali, yana mai cewa duk wanda ya yi wa wani kisan gilla ya kamata ya fuskanci hukuncin kisa.
Gagdi, wanda ya fito daga jihar Filto, ya ce duk wanda aka samu da laifin kisan kai ya kamata a aiwatar masa da hukuncin kisa maimakon a mayar da hankali kan gyara halinsa.
Ya bayyana hakan ne a ranar Asabar yayin wata hira da ya yi a gidan rediyon Silverbird Rhythm 93.7 FM da ke Jos, inda ya jaddada cewa bai kamata a riƙa amfani da kuɗaɗen jama’a wajen gyaran halin mutanen da ake zargi da kisan kai ga jama’an da ba suji ba su gani ba. A cewarsa, irin wannan tsari ya takaita adalci kuma ba zai kawo karshen masu irin wannan aiki ba na ta’addanci.
A cewarsa, “Duk wani mai laifi, duk wanda ya kashe ran wani, bai kamata a fara tunanin gyara halinsa ba.”














