ADC Ta Rushe Shugabannin Jam’iyyar a Kano, Ta Naɗa Kwamitin RiƙoJam’iyyar ADC ta rushe kwamitin gudanarwa na jam’iyyar a Jihar Kano tare da naɗa kwamitin riƙo da zai kula da harkokin jam’iyyar har zuwa lokacin da za a gudanar da zaɓukan cikin gida na gaba.
An sanar da hakan ne a ranar Litinin a Kano ta bakin Mataimakiyar Shugaban Jam’iyyar ta Ƙasa mai kula da shiyyar Arewa maso Yamma, Najaatu Muhammad, yayin wani taron manema labarai da aka gudanar a Cibiyar ’Yan Jarida ta Kano.
Da take jawabi ga manema labarai, Hajiya Naja’atu Muhammad ta ce sabon kwamitin riƙon zai kasance ƙarƙashin jagorancin Umar Bala.
Ta bayyana cewa shugabancin jam’iyyar na ƙasa ne ya ɗauki wannan mataki bisa tanade-tanaden kundin tsarin mulkin jam’iyyar domin tabbatar da haɗin kai, ci gaba da gudanar da ayyukan jam’iyyar da kuma kiyaye mutuncin tsarin mulkinta a Jihar Kano.
A cewarta, rushe shugabannin jam’iyyar na jihar da kuma naɗa kwamitin riƙon bai kamata a ɗauke shi a matsayin nasarar wani ɓangare na jam’iyyar a kan wani ba, illa dai mataki ne da kundin tsarin mulkin jam’iyyar ya tanada domin magance wani yanayi na gudanarwa da ya taso a cikin jam’iyyar.













