ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, July 16, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Bankwana Da 2025: Kaunar Kasar Sin Ga Zaman Lafiyar Duniya Da Kiyaye Martabar Yankunanta

by Sulaiman
7 months ago

A shekarar 2025 da muke bankwana da ita a yau, kasar Sin ta taka muhimmiyar rawa a kokarin samar da zaman lafiya a duniya, ta hanyoyin diflomasiyya, kawo ci gaba, da inganta huldar mabambantan bangarori a daidai lokacin da rikice-rikicen kasa da kasa suka tsananta zuwa wani mataki da ba a ga irinsa a shekaru da dama ba.

Domin karfafa aza harsashin gina zaman lafiya mai dorewa, Sin ta gabatar da muhimman shawarwari ga duniya da suka kunshi: Shawarar Inganta Tsaron Duniya, da Shawarar Tsarin Ciyar Da Duniya Gaba, da Shirin Bunkasa Wayewar Kai A Duniya, da kuma Sabon Tsarin Inganta Jagorancin Duniya. Dukkan wadannan sun kawo muhimman dabaru na magance rikice-rikice daga tushe, daga bangaren rashin daidaito zuwa gibin shugabanci, kuma sun yi daidai da muhimman abubuwan da Majalisar Dinkin Duniya ta sa a gaba.

A cikin shekarar 2025, kasar Sin ta ba da karfi ga jaddada hadin gwiwar kasashe maimakon fito-na-fito. Kiran da Shugaba Xi Jinping ya yi ta maimaitawa na samar da tsaro na bai-daya da nuna adawa da siyasar danne wata kasa ya yi tasiri a duk fadin kasashe masu tasowa, wadanda suka kara samun damar fada-a-ji bisa goyon bayan babbar alakar diflomasiyya ta kasar Sin a duniya da kuma shiga a dama da su cikin harkokin yanki da na duniya baki daya.

ADVERTISEMENT

Rawar da kasar Sin ta taka a MDD kan dakatar da yakin Zirin Gaza, da kokarin ganin an sulhunta rikice-rikicen kasashe irin su Sudan, da Sudan ta Kudu, da Syria da kuma na baya-bayan nan tsakanin Cambodia da Thailand, duka sun nuna kaunarta ga zaman lafiya. Haka nan ta yi yekuwar tunatar da duniya muhimmancin kiyaye zaman lafiya, ta hanyar gudanar da bikin cika shekaru 80 da samun nasarar yaki da mamayar dakarun Japan da kuma yakin duniya na biyu.

Sai dai kuma, duk da kokarinta na tabbatar da dorewar zaman lafiyar duniya, zuwa karshen 2025, masu tsokanar fada kan batun Taiwan suna kokarin sake tayar da zaune tsaye, wadda kuma Sin ta nuna ba za ta bari wani ya zo har cikin gida ya yi mata sakiyar da ba ruwa ba.

LABARAI MASU NASABA

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

Sin ta yi amannar cewa, samun daumammen zaman lafiya na bukatar kare ’yancin kasa da kiyaye martabar yankunanta. Ta sha damarar mayar da martani mai gauni a kan ayyukan wuce gona da iri na ‘yan awaren Taiwan, tare da ’yan katsalandan da ke mara musu baya daga waje.

Atisayenta na soja a kwanan nan da kuma gargadinta mai karfi ta hanyar diflomasiyya ba abubuwa ne da suka saba wa yanayin zaman lafiyar duniya ba, sai dai matakai ne da suka wajaba ta dauka don hana fadada barazana da kuma tabbatar da ka’idar “Sin daya tilo a duniya”. Kazalika, ta dauki batun habaka zaman lafiya a duniya da kuma kare ’yancin martabatar yankunanta a matsayin wani nauyi da ba zai yiwu a raba su wajen saukewa ba. Kuma hakan ya tabbatar da tabarau da ta sa na “kifi na ganinka mai jar koma!” Da fatan ’yan tayar da zaune tsaye sun fahimci sakon kuma za su bari a shiga sabuwar shekarar 2026 cikin salama! (Abdulrazaq Yahuza Jere)

Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo
  • Sulaiman
    Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta
  • Sulaiman
    Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya
  • Sulaiman
    Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

MASU ALAKA

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo
Daga Birnin Sin

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

July 15, 2026
Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta
Daga Birnin Sin

Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

July 15, 2026
Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa
Daga Birnin Sin

Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

July 15, 2026
Next Post
’Yan Bindiga Sun Sace Matafiya 28 A Jihar Filato

'Yan Bindiga Sun Rage Kuɗin Fansar Matafiya 28 Da Suka Sace A Filato zuwa N30m

LABARAI MASU NASABA

Duk Da Sauye-Sauyen Tattalin Arziƙi Kashi 79% Na Ƴan Nijeriya Na Cikin Talauci – Bankin Duniya

Duk Da Sauye-Sauyen Tattalin Arziƙi Kashi 79% Na Ƴan Nijeriya Na Cikin Talauci – Bankin Duniya

July 16, 2026
M.A. Abubakar Ya Zaɓi Farouk Mustapha A Matsayin  Mataimakinsa

M.A. Abubakar Ya Zaɓi Farouk Mustapha A Matsayin Mataimakinsa

July 16, 2026
Saliba Zai Yi Jinyar Watanni 5 Bayan Raunin Da Ya Samu A Bayansa

Saliba Zai Yi Jinyar Watanni 5 Bayan Raunin Da Ya Samu A Bayansa

July 16, 2026
Kotu Ta Yanke Wa Wani Hukuncin Ɗaurin Shekara 7 Kan Tallan Wiwi A Kafafen Sada Zumunta

Kotu Ta Yanke Wa Wani Hukuncin Ɗaurin Shekara 7 Kan Tallan Wiwi A Kafafen Sada Zumunta

July 16, 2026
Tinubu Yana Zuba Kyawawan Ayyuka A Nijeriya – Ganduje

Ganduje Ya Buƙaci A Yi Siyasar Aƙida Domin Inganta Dimokuraɗiyya A Nijeriya

July 16, 2026
Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

July 15, 2026
Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

July 15, 2026
Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

July 15, 2026
Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

July 15, 2026
Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

July 15, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.