ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Bankwana Da 2025: Kaunar Kasar Sin Ga Zaman Lafiyar Duniya Da Kiyaye Martabar Yankunanta

by Sulaiman
8 months ago

A shekarar 2025 da muke bankwana da ita a yau, kasar Sin ta taka muhimmiyar rawa a kokarin samar da zaman lafiya a duniya, ta hanyoyin diflomasiyya, kawo ci gaba, da inganta huldar mabambantan bangarori a daidai lokacin da rikice-rikicen kasa da kasa suka tsananta zuwa wani mataki da ba a ga irinsa a shekaru da dama ba.

Domin karfafa aza harsashin gina zaman lafiya mai dorewa, Sin ta gabatar da muhimman shawarwari ga duniya da suka kunshi: Shawarar Inganta Tsaron Duniya, da Shawarar Tsarin Ciyar Da Duniya Gaba, da Shirin Bunkasa Wayewar Kai A Duniya, da kuma Sabon Tsarin Inganta Jagorancin Duniya. Dukkan wadannan sun kawo muhimman dabaru na magance rikice-rikice daga tushe, daga bangaren rashin daidaito zuwa gibin shugabanci, kuma sun yi daidai da muhimman abubuwan da Majalisar Dinkin Duniya ta sa a gaba.

A cikin shekarar 2025, kasar Sin ta ba da karfi ga jaddada hadin gwiwar kasashe maimakon fito-na-fito. Kiran da Shugaba Xi Jinping ya yi ta maimaitawa na samar da tsaro na bai-daya da nuna adawa da siyasar danne wata kasa ya yi tasiri a duk fadin kasashe masu tasowa, wadanda suka kara samun damar fada-a-ji bisa goyon bayan babbar alakar diflomasiyya ta kasar Sin a duniya da kuma shiga a dama da su cikin harkokin yanki da na duniya baki daya.

ADVERTISEMENT

Rawar da kasar Sin ta taka a MDD kan dakatar da yakin Zirin Gaza, da kokarin ganin an sulhunta rikice-rikicen kasashe irin su Sudan, da Sudan ta Kudu, da Syria da kuma na baya-bayan nan tsakanin Cambodia da Thailand, duka sun nuna kaunarta ga zaman lafiya. Haka nan ta yi yekuwar tunatar da duniya muhimmancin kiyaye zaman lafiya, ta hanyar gudanar da bikin cika shekaru 80 da samun nasarar yaki da mamayar dakarun Japan da kuma yakin duniya na biyu.

Sai dai kuma, duk da kokarinta na tabbatar da dorewar zaman lafiyar duniya, zuwa karshen 2025, masu tsokanar fada kan batun Taiwan suna kokarin sake tayar da zaune tsaye, wadda kuma Sin ta nuna ba za ta bari wani ya zo har cikin gida ya yi mata sakiyar da ba ruwa ba.

LABARAI MASU NASABA

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Sin ta yi amannar cewa, samun daumammen zaman lafiya na bukatar kare ’yancin kasa da kiyaye martabar yankunanta. Ta sha damarar mayar da martani mai gauni a kan ayyukan wuce gona da iri na ‘yan awaren Taiwan, tare da ’yan katsalandan da ke mara musu baya daga waje.

Atisayenta na soja a kwanan nan da kuma gargadinta mai karfi ta hanyar diflomasiyya ba abubuwa ne da suka saba wa yanayin zaman lafiyar duniya ba, sai dai matakai ne da suka wajaba ta dauka don hana fadada barazana da kuma tabbatar da ka’idar “Sin daya tilo a duniya”. Kazalika, ta dauki batun habaka zaman lafiya a duniya da kuma kare ’yancin martabatar yankunanta a matsayin wani nauyi da ba zai yiwu a raba su wajen saukewa ba. Kuma hakan ya tabbatar da tabarau da ta sa na “kifi na ganinka mai jar koma!” Da fatan ’yan tayar da zaune tsaye sun fahimci sakon kuma za su bari a shiga sabuwar shekarar 2026 cikin salama! (Abdulrazaq Yahuza Jere)

Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5
  • Sulaiman
    Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana
  • Sulaiman
    ‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna
  • Sulaiman
    Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

MASU ALAKA

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5
Daga Birnin Sin

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana
Daga Birnin Sin

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi
Daga Birnin Sin

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Next Post
’Yan Bindiga Sun Sace Matafiya 28 A Jihar Filato

'Yan Bindiga Sun Rage Kuɗin Fansar Matafiya 28 Da Suka Sace A Filato zuwa N30m

LABARAI MASU NASABA

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

September 8, 2026
Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja

Kano Za Ta Kafa Sansanonin Sojoji A Ƙananan Hukumomin Da Ke Fuskantar Barazanar Tsaro

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.