Hukumar Kula da Asibitoci ta Jihar Kano ta tabbatar da cewa lamarin da ke da alaƙa da mutuwar, Aishatu Umar, ya faru ne a Cibiyar Kula da Cututtukan da suka shafi mafitsara ta Abubakar Imam, bayan zarge-zargen sakaci a fannin lafiya wanda ya haifar da fushin jama’a da Allah-wadai daga al’ummimi a fadin jihar Kano.
A cikin wata sanarwa da ta fitar a ranar Talata da yamma wacce Jami’ar Hulɗa da Jama’a ta Hukumar, Samira Suleiman ta sanya wa hannu, Hukumar ta ce, binciken farko wanda Sakataren Gudanarwarta, Dr. Mansur Mudi Nagoda ya umarta, “ya tabbatar da cewa, lamarin ya faru da marigayiya Aishatu Umar ne a Cibiyar Kula da Cututtukan mafitsara ta Abubakar Imam.”
Sanarwar ta ce bisa ga jajircewar Hukumar na daukar matakan hukunci, “an dakatar da ma’aikata uku (3) da ke da hannu kai tsaye a lamarin daga ayyukan asibiti nan take.”
Ta kuma kara da cewa, an tura lamarin zuwa Kwamitin Da’a na Lafiya na Jihar Kano don ƙarin bincike da kuma yiwuwar ɗaukar matakin ladabtarwa. A cewar Hukumar, an tura lamarin ne don tabbatar da “daukar matakin ladabtarwa daidai da tanadin dokar aikin kwararrun likitoci.”
Daga karshe, Hukumar ta mika ta’aziyyarta ga iyalan marigayiya Aishatu Umar, sannan ta kuma tabbatar wa jama’a cewa “ba za ta lamunci sakaci a aiki ta kowace hanya ba.”















Discussion about this post