ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, June 24, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Matsalolin Gidan Aure Da Yadda Za A Gyara (1)

by Bilkisu Tijjani
2 years ago
Aure

Rashin Dawowar Maigida Da Wuri

Assalamu alaikum masu karatu barkanmu da sake haduwa da ku a wannan makon a shafin Uwargida Sarautar mata. A yau shafin na mu zai zo muku da abubuwan da ke kawo matsala a gidan aure. Masu hikima kan ce “idan an san matsala, to an samu rabin maganinta”. Don haka ya kamata mu fahimci asalin matsalolin da ke addabar mu a gidajen aure domin ya ba mu damar sanin ta inda za mu fara magancewa.

Matsalar Farko

ADVERTISEMENT

Rashin Dawowar Maigida Da Wuri: Wannan matsala ce da na san tana matukar ci wa mata da yawa tuwo a kwarya. Watakila mijinki ma’aikaci ne, ya fita tun safe bai dawo da rana ba, don haka uwargida za ta zaku ta ga maigida ya dawo kafin Magriba. Amma kuma wasu sai bayan Sallar Isha’i suke dawowa. Uwargida ta caba ado tana ta jira har bacci ya fara neman rinjayar ta. Irin wannan matsala ce gaskiya babba a cikin zaman aure. Domin magancewa, yana da kyau uwargida ki fara duba wadannan abubuwan, kina yi ko dai kin rungume hannu ne kina ta cika kina batsewa ke kadai?

Shin yaya yake fita daga gidanki, kina kokarin kin saka shi a cikin farin ciki da annashuwa kafin ya fita ko dai da fada kuke rabuwa? Ya kama uwargida kisan cewa kafin maigida ya fita kin yi kokarin yadda za ki sa shi ya fita yana farin ciki, kin yi abinci ya ci, kin shirya shi, wato ina nufin za ki iya yi wa mijinki wanka ki shafa masa mai kin sa masa kaya ki hula ki sa idan ba mai amfani da suit bane, idan mai sa suit ne ki tabbatar kin iya yadda ake kayan suit kin iya daura belt ki sa masa safa da takalmi ya fito tsaf ki kamo hannunsa ki raka shi idan mai mota ne ki kai shi har mota ki bude masa ya shiga ki masa fatan alkhairi tare da addu’ar samun nasara ki gani kafin a tashi a wajen aiki zai rika matsuwa a yi a tashi saboda ya koma gida.

LABARAI MASU NASABA

An Nemi Shugabanni Su Rungumi Tafarkin Adalci A Tsakanin Al’ummunsu

Ƴan Bindiga Sun Tilasta Wa Ƙauyukan Sakkwato Biyan Sabon Haraji

 Shin idan ya fita wane irin sako kike aika masa? Ko dai ke ‘yar ba ruwana ce da me cewa idan aka biye wa namiji babu abin da za a kulla a rayuwa? Kin yi shiru, kin kyale maigida ko tunawa da shi ba kya yi ballantana ki aika masa da dadaddan sakonni da zai sa ya ji shi kansa ya zaku ya dawo gida kuma abin Allah ya kiyaye, wata tana can tana tunani da zakulo sabbin dabarun sace zuciyarsa ke kuma kin zauna shiru, an ya kuwa a haka yaki ba zai ciki ba? Yana da kyau ki rika aika masa da sakonni da za su nuna masa cewa shi ne fa a gaban ki kuma tabbas yana da wadda ta damu da shi. Ba kiran waya za ki rika yi ba a kai a kai, a’a, watakila wani aikinsa ba ya son haka, amma sako, duk lokacin da ya samu sarari zai duba.

 Abu na gaba shi ne, yaya kike karbarsa idan ya dawo gida kuma a wane hali yake samunki, ya yanayin gidanki yake, ya makwancinsa yake? Na tabbatar da cewa duk wadannan tambayoyin kin san amsarsu, abin da ya rage shi ne ki kimtsa masa kanki, kar ki tarbe shi da kayan da kika yi girki a jikinki, ki gyara gidanki, ki kimtsa yara tsaf sannan da ya shiga daki ya tarar da abin da zai kara kwantar masa da hankali cewa lallai ya dawo gida, wato ki iya shimfada kado wani namijin shimfida kado kadai tana kwantar masa da hankali yaji yana san wannan mai shimfadar a kusa da shi amma da yawa wasu matan basu iya shimfadar gado ba sai ki ga can zanin gado ya cikorkode can ya shamide, wata kuma daga ranar da ta sake zanin gado ba za ta sake shimfada ba sai randa ya yi datti za ta canja wani, lailaya shimfadar gado tanajan hankalin namiji sosai ya ji zai huta ba zai so ya tashi ba, wata kuwa ko kayan da ya je akan gadon ba za ta dauke ba har sai sanda ya dauke abin sa saboda ba ta damu da gyaran gadon ba.

Aure
Bilkisu Tijjani
+ postsBio
  • Bilkisu Tijjani
    https://hausa.leadership.ng/author/bilkisu-tijjani/
    Yadda Ake Wainar Masara Da Miyar Yaji
  • Bilkisu Tijjani
    https://hausa.leadership.ng/author/bilkisu-tijjani/
    Hanyoyin Hada Humra Mai Kamshi
  • Bilkisu Tijjani
    https://hausa.leadership.ng/author/bilkisu-tijjani/
    Yadda Ake Miyar Margi Da Kifin Tarwad
  • Bilkisu Tijjani
    https://hausa.leadership.ng/author/bilkisu-tijjani/
    A Matsayinki Na Mace, Kada Ki Yi Wasa Da Wadannan Abubuwa

MASU ALAKA

Nijeriya
Rahotonni

An Nemi Shugabanni Su Rungumi Tafarkin Adalci A Tsakanin Al’ummunsu

June 20, 2026
Ambaliyar Ruwa Ta Lalata Gidaje 14,940 A Sokoto
Rahotonni

Ƴan Bindiga Sun Tilasta Wa Ƙauyukan Sakkwato Biyan Sabon Haraji

June 20, 2026
IMF
Rahotonni

Tattalin Arziƙin Ƙasa: Masana Sun Buƙaci Tinubu Ya Yi Hattara Da Shawarar IMF

June 20, 2026
Next Post
Tarihin Masarautar Zazzau Da Sarakunanta (8)

Tarihin Masarautar Zazzau Da Sarakunanta (8)

LABARAI MASU NASABA

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.