ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Matsalolin Gidan Aure Da Yadda Za A Gyara (1)

by Bilkisu Tijjani
2 years ago
Aure

Rashin Dawowar Maigida Da Wuri

Assalamu alaikum masu karatu barkanmu da sake haduwa da ku a wannan makon a shafin Uwargida Sarautar mata. A yau shafin na mu zai zo muku da abubuwan da ke kawo matsala a gidan aure. Masu hikima kan ce “idan an san matsala, to an samu rabin maganinta”. Don haka ya kamata mu fahimci asalin matsalolin da ke addabar mu a gidajen aure domin ya ba mu damar sanin ta inda za mu fara magancewa.

Matsalar Farko

ADVERTISEMENT

Rashin Dawowar Maigida Da Wuri: Wannan matsala ce da na san tana matukar ci wa mata da yawa tuwo a kwarya. Watakila mijinki ma’aikaci ne, ya fita tun safe bai dawo da rana ba, don haka uwargida za ta zaku ta ga maigida ya dawo kafin Magriba. Amma kuma wasu sai bayan Sallar Isha’i suke dawowa. Uwargida ta caba ado tana ta jira har bacci ya fara neman rinjayar ta. Irin wannan matsala ce gaskiya babba a cikin zaman aure. Domin magancewa, yana da kyau uwargida ki fara duba wadannan abubuwan, kina yi ko dai kin rungume hannu ne kina ta cika kina batsewa ke kadai?

Shin yaya yake fita daga gidanki, kina kokarin kin saka shi a cikin farin ciki da annashuwa kafin ya fita ko dai da fada kuke rabuwa? Ya kama uwargida kisan cewa kafin maigida ya fita kin yi kokarin yadda za ki sa shi ya fita yana farin ciki, kin yi abinci ya ci, kin shirya shi, wato ina nufin za ki iya yi wa mijinki wanka ki shafa masa mai kin sa masa kaya ki hula ki sa idan ba mai amfani da suit bane, idan mai sa suit ne ki tabbatar kin iya yadda ake kayan suit kin iya daura belt ki sa masa safa da takalmi ya fito tsaf ki kamo hannunsa ki raka shi idan mai mota ne ki kai shi har mota ki bude masa ya shiga ki masa fatan alkhairi tare da addu’ar samun nasara ki gani kafin a tashi a wajen aiki zai rika matsuwa a yi a tashi saboda ya koma gida.

LABARAI MASU NASABA

Ko Yakin Iran Zai Kawo Karshen Kawancen Amurka Da Kasashen Larabawa?

Yadda Sauya Shekar ‘Yan Siyasa Ta Sauya Fasalin Majalisar Dokokin Kasa

 Shin idan ya fita wane irin sako kike aika masa? Ko dai ke ‘yar ba ruwana ce da me cewa idan aka biye wa namiji babu abin da za a kulla a rayuwa? Kin yi shiru, kin kyale maigida ko tunawa da shi ba kya yi ballantana ki aika masa da dadaddan sakonni da zai sa ya ji shi kansa ya zaku ya dawo gida kuma abin Allah ya kiyaye, wata tana can tana tunani da zakulo sabbin dabarun sace zuciyarsa ke kuma kin zauna shiru, an ya kuwa a haka yaki ba zai ciki ba? Yana da kyau ki rika aika masa da sakonni da za su nuna masa cewa shi ne fa a gaban ki kuma tabbas yana da wadda ta damu da shi. Ba kiran waya za ki rika yi ba a kai a kai, a’a, watakila wani aikinsa ba ya son haka, amma sako, duk lokacin da ya samu sarari zai duba.

 Abu na gaba shi ne, yaya kike karbarsa idan ya dawo gida kuma a wane hali yake samunki, ya yanayin gidanki yake, ya makwancinsa yake? Na tabbatar da cewa duk wadannan tambayoyin kin san amsarsu, abin da ya rage shi ne ki kimtsa masa kanki, kar ki tarbe shi da kayan da kika yi girki a jikinki, ki gyara gidanki, ki kimtsa yara tsaf sannan da ya shiga daki ya tarar da abin da zai kara kwantar masa da hankali cewa lallai ya dawo gida, wato ki iya shimfada kado wani namijin shimfida kado kadai tana kwantar masa da hankali yaji yana san wannan mai shimfadar a kusa da shi amma da yawa wasu matan basu iya shimfadar gado ba sai ki ga can zanin gado ya cikorkode can ya shamide, wata kuma daga ranar da ta sake zanin gado ba za ta sake shimfada ba sai randa ya yi datti za ta canja wani, lailaya shimfadar gado tanajan hankalin namiji sosai ya ji zai huta ba zai so ya tashi ba, wata kuwa ko kayan da ya je akan gadon ba za ta dauke ba har sai sanda ya dauke abin sa saboda ba ta damu da gyaran gadon ba.

Aure
Bilkisu Tijjani
+ postsBio
  • Bilkisu Tijjani
    https://hausa.leadership.ng/author/bilkisu-tijjani/
    Nasihar Da Ya Dace Dukkan Iyaye Su Yi Wa ‘Yaƴansu Yayin  Aure?
  • Bilkisu Tijjani
    https://hausa.leadership.ng/author/bilkisu-tijjani/
    Abin Da Yake Kashe Matanmu Na Hausawa
  • Bilkisu Tijjani
    https://hausa.leadership.ng/author/bilkisu-tijjani/
    Kafin Ki Nemi Saki, Nemi Amsar Waɗannan Tambayoyi Da Kanki
  • Bilkisu Tijjani
    https://hausa.leadership.ng/author/bilkisu-tijjani/
    Ko Kin San… Cututtukan Da Man Ridi Ke Warkarwa?

MASU ALAKA

Aure
Rahotonni

Ko Yakin Iran Zai Kawo Karshen Kawancen Amurka Da Kasashen Larabawa?

May 17, 2026
Aure
Rahotonni

Yadda Sauya Shekar ‘Yan Siyasa Ta Sauya Fasalin Majalisar Dokokin Kasa

May 16, 2026
Abincin Da Ya Kamata Ku Ci Lokacin Al’ada
Rahotonni

Almajiranci:Matsala Ko Maslaha

May 10, 2026
Next Post
Tarihin Masarautar Zazzau Da Sarakunanta (8)

Tarihin Masarautar Zazzau Da Sarakunanta (8)

LABARAI MASU NASABA

Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.