ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, June 5, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Bikin CIIE Karo Na 7: Yadda Kara Shigowar Afirka A Dama Da Ita Ya Birge Matuka

by CGTN Hausa and Sulaiman
2 years ago
CIIE

A kwanan ne aka kamala bikin baje kolin kayayyakin da ake shigowa da su kasar Sin karo na 7 wanda ya kasance daya daga cikin manyan hikimomin da kasar Sin ta bullo da su a karkashin shirinta na kara bude kofar hulda da sauran sassan duniya.

 

Na kalla ta talabijin yadda wasu mahukunta da shugabannin kamfanoni da na ’yan kasuwa daban-daban na kasashen duniya daga wasu sassan da ba na Afirka ba suke bayyana alfanun wannan biki ga ci gabansu. Abin ya zama gwanin ban-sha’awa amma dai, tun da ban yi katarin ganin na Afirka ba sai na ba zama tare da raba na-mujiya a kafafen yada labarai don zakulo yadda mutanenmu suka shiga aka dama da su.

ADVERTISEMENT
  • Salon Zamanantarwa Irin Na Kasar Sin Riba Ce Ga Duniya Baki Daya
  • Ya Kamata Rungumar Hadin Gwiwa Da Yin Komai A Bude Su Zamo Ginshikan Ci Gaban Yankin Asiya Da Pacifik A Nan Gaba

Watakila mai karatu ya ce, me ya sa na damu da sai na ga na Afirka, e, dole na damu, domin na ji cewa a bisa karamci, matakan inganta harkokin kasuwanci da kasar Sin ta dauka sun kara habaka kayayyakin da Afirka ke fitarwa zuwa kasuwanninta ainun. A cikin watanni 9 na farkon bana, kayayyakin da kasar Sin ta shigo da su daga Afirka sun kai adadin yuan biliyan 626.74 kwatankwacin dalar Amurka biliyan 87, wanda ya nuna an samu karuwar kashi 10.3 cikin 100 a mizanin da ake aunawa duk shekara, kamar yadda hukumar kwastam ta kasar Sin ta bayyana. Ka ga kuwa dole na bibiyi na mutanenmu na gani tun da an ce “da arziki a gidan wasu, gwara a gidanku.”

 

LABARAI MASU NASABA

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

Daga shawagin da na yi a kafafen labarai, na yi kicibis da tsokacin da ’yan Afirka da suka halarci bikin baje kolin na CIIE na bana suka yi. Wani dan Nijeriya, Usman Sa’id Sufi, bayan jinjina wa kasar Sin a kan yadda take bude kofofinta ga daukacin duniya bisa adalcin kasuwanci, ya ce, a bana sun baje hajojinsu na Nijeriya da suka kunshi kayan noma da ma’adanan kasa. Yana mai cewar, “mun kawo kamar ridi, da sobarodo (ganyen zobo), kwallon tafasa, garin rogo, gyada, cashew (yazawa), karo, waken suya da sauran kayayyaki kala-kala.”

 

Daga kasar Afirka ta Kudu kuwa, wani dan kasuwa da ya halarci bikin a karon farko tare da baje kolin kayan lambu na avocado, Nkateko Khoza ya bayyana cewa kasuwar kasar Sin za ta kawo sabbin damammaki na bunkasa masana’antar avocado ta kasar Afirka ta Kudu, inda ya kara da cewa, wannan damar za ta bai wa kamfaninsu na noma mai suna Khoza Farming damar ninka ci gaban da yake samu a cikin shekaru uku zuwa biyar masu zuwa.

 

Wani abin ban-shawa da ke kara nuna yadda Afirka ke shiga a dama da ita a kasuwar baje kolin ta CIIE shi ne, wannan ne karo na farko da ake baje kolin naman kosassun raguna na kasar Madagascar. Amma kafin nan, kasar Sin ta riga ta shigo da irin wannan naman na farko daga Afirka a watan Satumbar bana, bayan da hukumar kwastan ta Changsha da ke tsakiyar kasar Sin ta tantance ingancin naman na Madagascar. A cewar Babban Daraktan Noma da Kiwo na Ma’aikatar Noma ta Madagascar, Michel Anondraka, babbar kasuwar kasar Sin za ta bunkasa harkokin noma da kiwo ga manoman gida, tare da gaggauta zamanantar da aikin gona na yankin Afirka.

 

Haka nan duk dai a bikin na CIIE na bana ne aka fara baje kolin zumar da kasar Tanzaniya ke samarwa. Kuma bisa yakinin Babban Manajan Kamfanin Sarrafa Zuma da Samar da Kayayyakin Kiwonsa na Tanzania Future Enterprises Company Limited, Jackson Mponela, “Wannan baje kolin wata babbar dama ce ga harkokin kasuwancin zuma a fadin Tanzaniya, domin ba wai kawai ya share fagen shiga kasuwannin kasar Sin ne kadai ba, har ma ya zama wani muhimmin mataki ga cinikayyar zumar Tanzaniya a kasuwannin duniya.”

 

Wadannan kadan ne daga cikin misalan kara shigowar Afirka a dama da ita a bikin baje kolin CIIE na bana kuma tabbas, karamcin da kasar Sin ta yi wa kasashen Afirka 33 da suke huldar diflomasiyya tare cewa ta cire musu harajin halartar kasuwar baje kolin, zai kara musu kaimi da kuma cin moriyar juna.

 

A kalla shugabannin gwamnatoci da kamfanoni da kungiyoyin ’yan kasuwa daban-daban na duniya 77 ne suka halarci bikin baje kolin na CIIE na bana. (Abdulrazaq Yahuza Jere)

CIIE
CGTN Hausa
+ posts Bio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku
CIIE
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya
  • Sulaiman
    Gwamna Sani Ya Kashe Sama Da Naira Biliyan Ɗaya Kan Tallafin Ɗalibai A Kaduna – Kwamishina
  • Sulaiman
    Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026
  • Sulaiman
    Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

MASU ALAKA

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya
Daga Birnin Sin

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

June 4, 2026
Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026
Daga Birnin Sin

Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

June 4, 2026
Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci
Daga Birnin Sin

Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

June 4, 2026
Next Post
Mutfwang Ya Amince Da Mafi Karancin Albashi Na N70,000 Ga Ma’aikatan Filato

Mutfwang Ya Amince Da Mafi Karancin Albashi Na N70,000 Ga Ma'aikatan Filato

LABARAI MASU NASABA

Matatar Dangote Ta Ƙara Yawan Man Da Take Tacewa Zuwa Ganga 700,000

Matatar Dangote Ta Ƙara Yawan Man Da Take Tacewa Zuwa Ganga 700,000

June 4, 2026
Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

June 4, 2026
Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

June 4, 2026
Mun Kaɗu Matuƙa Kan Labarin Mutuwar ‘Yan Mauludi A Hanyar Saminaka – Gwamnan Kaduna

Gwamna Sani Ya Kashe Sama Da Naira Biliyan Ɗaya Kan Tallafin Ɗalibai A Kaduna – Kwamishina

June 4, 2026
Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

June 4, 2026
Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

June 4, 2026
Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

June 4, 2026
Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

June 4, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.