ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, July 17, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Bikin CIIE Karo Na 7: Yadda Kara Shigowar Afirka A Dama Da Ita Ya Birge Matuka

by CGTN Hausa and Sulaiman
2 years ago
CIIE

A kwanan ne aka kamala bikin baje kolin kayayyakin da ake shigowa da su kasar Sin karo na 7 wanda ya kasance daya daga cikin manyan hikimomin da kasar Sin ta bullo da su a karkashin shirinta na kara bude kofar hulda da sauran sassan duniya.

 

Na kalla ta talabijin yadda wasu mahukunta da shugabannin kamfanoni da na ’yan kasuwa daban-daban na kasashen duniya daga wasu sassan da ba na Afirka ba suke bayyana alfanun wannan biki ga ci gabansu. Abin ya zama gwanin ban-sha’awa amma dai, tun da ban yi katarin ganin na Afirka ba sai na ba zama tare da raba na-mujiya a kafafen yada labarai don zakulo yadda mutanenmu suka shiga aka dama da su.

ADVERTISEMENT
  • Salon Zamanantarwa Irin Na Kasar Sin Riba Ce Ga Duniya Baki Daya
  • Ya Kamata Rungumar Hadin Gwiwa Da Yin Komai A Bude Su Zamo Ginshikan Ci Gaban Yankin Asiya Da Pacifik A Nan Gaba

Watakila mai karatu ya ce, me ya sa na damu da sai na ga na Afirka, e, dole na damu, domin na ji cewa a bisa karamci, matakan inganta harkokin kasuwanci da kasar Sin ta dauka sun kara habaka kayayyakin da Afirka ke fitarwa zuwa kasuwanninta ainun. A cikin watanni 9 na farkon bana, kayayyakin da kasar Sin ta shigo da su daga Afirka sun kai adadin yuan biliyan 626.74 kwatankwacin dalar Amurka biliyan 87, wanda ya nuna an samu karuwar kashi 10.3 cikin 100 a mizanin da ake aunawa duk shekara, kamar yadda hukumar kwastam ta kasar Sin ta bayyana. Ka ga kuwa dole na bibiyi na mutanenmu na gani tun da an ce “da arziki a gidan wasu, gwara a gidanku.”

 

LABARAI MASU NASABA

Pew: Sin Ta fi Amurka Samun Amincewar Al’ummun Duniya

Sin Ta Fitar Da Tsarin Sanya Ido Don Inganta Muhalli Da Muhallin Halittu Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

Daga shawagin da na yi a kafafen labarai, na yi kicibis da tsokacin da ’yan Afirka da suka halarci bikin baje kolin na CIIE na bana suka yi. Wani dan Nijeriya, Usman Sa’id Sufi, bayan jinjina wa kasar Sin a kan yadda take bude kofofinta ga daukacin duniya bisa adalcin kasuwanci, ya ce, a bana sun baje hajojinsu na Nijeriya da suka kunshi kayan noma da ma’adanan kasa. Yana mai cewar, “mun kawo kamar ridi, da sobarodo (ganyen zobo), kwallon tafasa, garin rogo, gyada, cashew (yazawa), karo, waken suya da sauran kayayyaki kala-kala.”

 

Daga kasar Afirka ta Kudu kuwa, wani dan kasuwa da ya halarci bikin a karon farko tare da baje kolin kayan lambu na avocado, Nkateko Khoza ya bayyana cewa kasuwar kasar Sin za ta kawo sabbin damammaki na bunkasa masana’antar avocado ta kasar Afirka ta Kudu, inda ya kara da cewa, wannan damar za ta bai wa kamfaninsu na noma mai suna Khoza Farming damar ninka ci gaban da yake samu a cikin shekaru uku zuwa biyar masu zuwa.

 

Wani abin ban-shawa da ke kara nuna yadda Afirka ke shiga a dama da ita a kasuwar baje kolin ta CIIE shi ne, wannan ne karo na farko da ake baje kolin naman kosassun raguna na kasar Madagascar. Amma kafin nan, kasar Sin ta riga ta shigo da irin wannan naman na farko daga Afirka a watan Satumbar bana, bayan da hukumar kwastan ta Changsha da ke tsakiyar kasar Sin ta tantance ingancin naman na Madagascar. A cewar Babban Daraktan Noma da Kiwo na Ma’aikatar Noma ta Madagascar, Michel Anondraka, babbar kasuwar kasar Sin za ta bunkasa harkokin noma da kiwo ga manoman gida, tare da gaggauta zamanantar da aikin gona na yankin Afirka.

 

Haka nan duk dai a bikin na CIIE na bana ne aka fara baje kolin zumar da kasar Tanzaniya ke samarwa. Kuma bisa yakinin Babban Manajan Kamfanin Sarrafa Zuma da Samar da Kayayyakin Kiwonsa na Tanzania Future Enterprises Company Limited, Jackson Mponela, “Wannan baje kolin wata babbar dama ce ga harkokin kasuwancin zuma a fadin Tanzaniya, domin ba wai kawai ya share fagen shiga kasuwannin kasar Sin ne kadai ba, har ma ya zama wani muhimmin mataki ga cinikayyar zumar Tanzaniya a kasuwannin duniya.”

 

Wadannan kadan ne daga cikin misalan kara shigowar Afirka a dama da ita a bikin baje kolin CIIE na bana kuma tabbas, karamcin da kasar Sin ta yi wa kasashen Afirka 33 da suke huldar diflomasiyya tare cewa ta cire musu harajin halartar kasuwar baje kolin, zai kara musu kaimi da kuma cin moriyar juna.

 

A kalla shugabannin gwamnatoci da kamfanoni da kungiyoyin ’yan kasuwa daban-daban na duniya 77 ne suka halarci bikin baje kolin na CIIE na bana. (Abdulrazaq Yahuza Jere)

CIIE
CGTN Hausa
+ posts Bio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Pew: Sin Ta fi Amurka Samun Amincewar Al’ummun Duniya
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Sin Ta Fitar Da Tsarin Sanya Ido Don Inganta Muhalli Da Muhallin Halittu Na Shekarar 2026 Zuwa 2030
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    An Yi Bikin Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Kafa Kungiyar Hadin Gwiwar Fasahar AI Ta Duniya A Shanghai
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Ra’yin Sin Da Afirka Ya Zo Daya A Fannin Fasahar AI
CIIE
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Pew: Sin Ta fi Amurka Samun Amincewar Al’ummun Duniya
  • Sulaiman
    Sin Ta Fitar Da Tsarin Sanya Ido Don Inganta Muhalli Da Muhallin Halittu Na Shekarar 2026 Zuwa 2030
  • Sulaiman
    Nazari Game Da Damammakin Da Sin Ta Samar Cikin Rahoton Ci Gaban Tattalin Arzikinta Na Rabin Farkon Shekara
  • Sulaiman
    Gwamna Bala Ya Rushe Kwamitin Gudanarwar Wikki Tourists Bayan Rashin Nasararta A Gasar NPFL

MASU ALAKA

Pew: Sin Ta fi Amurka Samun Amincewar Al’ummun Duniya
Daga Birnin Sin

Pew: Sin Ta fi Amurka Samun Amincewar Al’ummun Duniya

July 16, 2026
Sin Ta Fitar Da Tsarin Sanya Ido Don Inganta Muhalli Da Muhallin Halittu Na Shekarar 2026 Zuwa 2030
Daga Birnin Sin

Sin Ta Fitar Da Tsarin Sanya Ido Don Inganta Muhalli Da Muhallin Halittu Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

July 16, 2026
Nazari Game Da Damammakin Da Sin Ta Samar Cikin Rahoton Ci Gaban Tattalin Arzikinta Na Rabin Farkon Shekara
Daga Birnin Sin

Nazari Game Da Damammakin Da Sin Ta Samar Cikin Rahoton Ci Gaban Tattalin Arzikinta Na Rabin Farkon Shekara

July 16, 2026
Next Post
Mutfwang Ya Amince Da Mafi Karancin Albashi Na N70,000 Ga Ma’aikatan Filato

Mutfwang Ya Amince Da Mafi Karancin Albashi Na N70,000 Ga Ma'aikatan Filato

LABARAI MASU NASABA

Pew: Sin Ta fi Amurka Samun Amincewar Al’ummun Duniya

Pew: Sin Ta fi Amurka Samun Amincewar Al’ummun Duniya

July 16, 2026
Sin Ta Fitar Da Tsarin Sanya Ido Don Inganta Muhalli Da Muhallin Halittu Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

Sin Ta Fitar Da Tsarin Sanya Ido Don Inganta Muhalli Da Muhallin Halittu Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

July 16, 2026
Nazari Game Da Damammakin Da Sin Ta Samar Cikin Rahoton Ci Gaban Tattalin Arzikinta Na Rabin Farkon Shekara

Nazari Game Da Damammakin Da Sin Ta Samar Cikin Rahoton Ci Gaban Tattalin Arzikinta Na Rabin Farkon Shekara

July 16, 2026
Gwamna Bala Ya Rushe Kwamitin Gudanarwar Wikki Tourists Bayan Rashin Nasararta A Gasar NPFL

Gwamna Bala Ya Rushe Kwamitin Gudanarwar Wikki Tourists Bayan Rashin Nasararta A Gasar NPFL

July 16, 2026
Tasirin Da Sabbin Hare-haren Amurka Da Iran Za Su Iya Haifarwa Duniya

Tasirin Da Sabbin Hare-haren Amurka Da Iran Za Su Iya Haifarwa Duniya

July 16, 2026
Sin Na Kokarin Sanya Ci Gaban Fasaha Ya Inganta Bunkasa Da Wadatar Dan Adam

Sin Na Kokarin Sanya Ci Gaban Fasaha Ya Inganta Bunkasa Da Wadatar Dan Adam

July 16, 2026
Tinubu Ya Miƙa Wa Shettima Takardar Tabbatar Da Shi Abokin Takararsa A Zaɓen 2027

Tinubu Ya Miƙa Wa Shettima Takardar Tabbatar Da Shi Abokin Takararsa A Zaɓen 2027

July 16, 2026
Xi Jinping Ya Gana Da Shugaban Kazakhstan

Xi Jinping Ya Gana Da Shugaban Kazakhstan

July 16, 2026
Mutfwang Ya Buƙaci Sojoji Su Ƙara Ƙaimi A Aikinsu

Mutfwang Ya Buƙaci Sojoji Su Ƙara Ƙaimi A Aikinsu

July 16, 2026
An Yi Bikin Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Kafa Kungiyar Hadin Gwiwar Fasahar AI Ta Duniya A Shanghai

An Yi Bikin Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Kafa Kungiyar Hadin Gwiwar Fasahar AI Ta Duniya A Shanghai

July 16, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.