Yayin da Amurka da Iran suka amince da yarjejeniyar fahimtar juna, kuma alamun sassauci suka tabbata, a tashin hankalin da ya wakana tsawon sama da watanni uku tsakanin Amurka da Isra’ila da Iran, ana ganin dauki-ba-dadin da ya wakana, da fito-na-fito mai nasaba da batun mashigin Hormuz, dukkaninsu ba su shaida wata nasara da Amurka ta yi aniyar samu ba.
Sakamakon wani binciken jin ra’ayoyin jama’a da kafar CGTN ta Sin ta gudanar, ya nuna yadda kaso 90.8 bisa dari na masu bayyana ra’ayoyin suka amince, cewa gwamnatin Amurka ta gaza cimma burikan da ta kuduri aniyar samu, wanda kuma hakan ya kara fallasa hakikanin halin da kasar ke ciki na raguwar tasirinta cikin harkokin duniya.
Kazalika, kaso 93.0 bisa dari na masu bayyana ra’ayoyin sun ce jerin matakai da Amurka ta aiwatar, da manufofi masu haifar da hargitsi ga batun Falasdinu da Isra’ila da Iran, su ne suka kara ingiza koma bayan yanayin tsaro a Gabas ta Tsakiya. Kana kaso 93.4 bisa dari na masu bayyana ra’ayoyin sun amince cewa tashin hankalin da ya auku, ya kara gaggauta rage tasirin Amurka a Gabas ta Tsakiya. (Saminu Alhassan)














Discussion about this post