ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, July 29, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamna Sule Ya Halarci Ƙaddamar da Kamfanin Jinlide•Qiangyu New Energy, Ya Ƙara Jaddada Aniyar Jawo Masu Zuba Jari

by Zubairu M Lawal and Sulaiman
11 hours ago
Gwamna Sule

Gwamnan Jihar Nasarawa, Injiniya Abdullahi Sule, ya halarci bikin ƙaddamar da Kamfanin Jinlide•Qiangyu New Energy a birnin Nanchang na lardin Jiangxi, a Kasar Sin, inda ya sake jaddada kudirin gwamnatinsa na ci gaba da jawo manyan masu zuba jari domin bunƙasa masana’antu da ƙara darajar albarkatun ma’adinan jihar Nasarawa.

Gwamnan ya halarci bikin tare da Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, inda ya bayyana ƙaddamar da katafaren kamfanin a matsayin wani muhimmin ci gaba da zai ƙara ƙarfafa haɗin gwiwar tattalin arziki tsakanin kamfanonin ƙasar Sin da jihohin Nijeriya masu albarkatun ma’adinai.

Da yake jawabi a wajen taron, Gwamna Sule ya yabawa shugabannin kamfanin bisa amincewar da suka nuna ga Nijeriya, yana mai cewa gwamnatin jihar za ta ci gaba da samar da yanayi mai kyau ga masu zuba jari ta hanyar aiwatar da manufofi masu gaskiya, inganta ababen more rayuwa da kuma tabbatar da gudanar da harkokin hakar ma’adinai bisa ƙa’ida.

ADVERTISEMENT

Ya ce manufar gwamnatinsa ita ce ƙarfafa kafa masana’antun da za su riƙa sarrafa albarkatun ma’adinai a cikin Jihar Nasarawa maimakon fitar da su a ɗanye, domin ƙara musu daraja, samar da ayyukan yi ga matasa, inganta musayar fasaha da kuma bunƙasa tattalin arzikin jihar da na ƙasa baki ɗaya.

Jajircewar gwamnatin Sule wajen inganta yanayin zuba jari ta fara haifar da sakamako, inda manyan kamfanonin ƙasar Sin suka fara kafa masana’antun sarrafa lithium a jihar. A shekarar 2024, Kamfanin Avatar New Energy ya ƙaddamar da masana’antar sarrafa lithium mai ƙarfin sarrafa tan 4,000 a kowace rana.

LABARAI MASU NASABA

Mun Yi Ƙoƙarin Sasanta Iran Da Amurka A Lokacin Gasar Kofin Duniya – Infantino

Ba Ma Fatan Wani Ɗan Nijeriya Ya Kwana da Yunwa — Remi Tinubu

Haka kuma, a ranar 2 ga Yuli, 2026, Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya ƙaddamar da katafaren Kamfanin Diamond New Energy da ke ƙaramar hukumar Nasarawa, wanda aka gina kan jarin dala miliyan 250 na Amurka. Kamfanin na da ƙarfin sarrafa tan 6,000 na lithium a kowace rana, kuma ana kallonsa a matsayin ɗaya daga cikin manyan masana’antun sarrafa lithium a Afirka.

Baya ga waɗannan, akwai wasu kamfanonin hakar lithium da dama da ke gudanar da ayyukansu a Jihar Nasarawa, lamarin da ya ƙara tabbatar da matsayin jihar a matsayin cibiyar masana’antar ma’adinai a Nijeriya.

A yayin ziyarar da ya kai Kamfanin Jinlide•Qiangyu New Energy, Gwamna Sule da tawagarsa sun zagaya sassa daban-daban na kamfanin, inda suka shaida yadda ake amfani da sabbin fasahohi wajen sarrafa kayayyaki tare da bin ƙa’idojin tabbatar da inganci.

Gwamnan ya bayyana gamsuwarsa da irin ci gaban fasahar da ya gani, yana mai cewa gwamnatin jihar za ta ci gaba da ƙarfafa haɗin gwiwa da kamfanonin ƙasar Sin tare da neman rattaba hannu kan ƙarin yarjejeniyoyin fahimtar juna domin faɗaɗa damar zuba jari a fannonin ma’adinai da masana’antu.

A ƙarshen bikin, shugabannin Kamfanin Jinlide•Qiangyu New Energy sun karrama Gwamna Abdullahi Sule da lambar yabo ta musamman saboda gudummawar da yake bayarwa wajen ƙarfafa haɗin gwiwar ƙasa da ƙasa da kuma jawo masu zuba jari zuwa Jihar Nasarawa.

Masu lura da al’amura na ganin cewa ci gaba da zuwan irin waɗannan manyan masana’antun zai taimaka wajen mayar da Jihar Nasarawa cibiyar sarrafa lithium da sauran muhimman ma’adinai a Nijeriya, tare da samar da dubban ayyukan yi da bunƙasa tattalin arziki mai ɗorewa.

Gwamna Sule
Zubairu M Lawal
+ posts Bio
  • Zubairu M Lawal
    https://hausa.leadership.ng/author/zubairu-m-lawal/
    Nasarawa Na Sa Ran Samun Dala Miliyan 10 Daga Lithium Kafin Karshen Shekara – Gwamna Sule
  • Zubairu M Lawal
    https://hausa.leadership.ng/author/zubairu-m-lawal/
    Mutane 600 Ne Kacal Suka Ci Jarabawar Ɗaukar Malaman Firamare Daga Cikin 8,000
  • Zubairu M Lawal
    https://hausa.leadership.ng/author/zubairu-m-lawal/
    Tinubu Ya Ƙaddamar Da Gadar Ƙasa Da Tituna A Akwanga
  • Zubairu M Lawal
    https://hausa.leadership.ng/author/zubairu-m-lawal/
    Gwamnatin Nasarawa Ta Rufe Kamfanin Haƙar Ma’adanai Saboda Rikicin Shari’a
Gwamna Sule
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Sin Ta Yi Martani Game Da Yiwuwar Kara Kudaden Da Amurka Ke Kashewa Da Nufin Dakile Tasirin Kasar Sin
  • Sulaiman
    Ma’aikatar Kasuwanci Ta Sin Ta Fitar Da Takarda Game Da Matsayin Sin Kan Abin Da Ake Kira “Samar Da Kayayyaki Fiye Da Kima”
  • Sulaiman
    Ba Ma Fatan Wani Ɗan Nijeriya Ya Kwana da Yunwa — Remi Tinubu
  • Sulaiman
    Kotun Ɗaukaka Ƙara Ta Soke Umarnin Cire Rajistar ADC Da Wasu Jam’iyyu Huɗu

MASU ALAKA

Mun Yi Ƙoƙarin Sasanta Iran Da Amurka A Lokacin Gasar Kofin Duniya – Infantino
Manyan Labarai

Mun Yi Ƙoƙarin Sasanta Iran Da Amurka A Lokacin Gasar Kofin Duniya – Infantino

July 29, 2026
Sana’ar Ƙosai: Remi Tinubu Ta Yi Kira ga Burna Boy da Davido Su Taimaka wa Talakawa
Labarai

Ba Ma Fatan Wani Ɗan Nijeriya Ya Kwana da Yunwa — Remi Tinubu

July 29, 2026
Ruwa
Manyan Labarai

2027: Gwamnan Kaduna Ya Sanar Da Sabon Mataimakinsa A Zaɓen Gwamna

July 28, 2026
Next Post
Sin Ta Yi Martani Game Da Yiwuwar Kara Kudaden Da Amurka Ke Kashewa Da Nufin Dakile Tasirin Kasar Sin

Sin Ta Yi Martani Game Da Yiwuwar Kara Kudaden Da Amurka Ke Kashewa Da Nufin Dakile Tasirin Kasar Sin

LABARAI MASU NASABA

Cinikin Salah Zuwa Besiktas Ya Rushe

Cinikin Salah Zuwa Besiktas Ya Rushe

July 29, 2026
Mun Yi Ƙoƙarin Sasanta Iran Da Amurka A Lokacin Gasar Kofin Duniya – Infantino

Mun Yi Ƙoƙarin Sasanta Iran Da Amurka A Lokacin Gasar Kofin Duniya – Infantino

July 29, 2026
Sin Ta Yi Martani Game Da Yiwuwar Kara Kudaden Da Amurka Ke Kashewa Da Nufin Dakile Tasirin Kasar Sin

Sin Ta Yi Martani Game Da Yiwuwar Kara Kudaden Da Amurka Ke Kashewa Da Nufin Dakile Tasirin Kasar Sin

July 29, 2026
Gwamna Sule Ya Halarci Ƙaddamar da Kamfanin Jinlide•Qiangyu New Energy, Ya Ƙara Jaddada Aniyar Jawo Masu Zuba Jari

Gwamna Sule Ya Halarci Ƙaddamar da Kamfanin Jinlide•Qiangyu New Energy, Ya Ƙara Jaddada Aniyar Jawo Masu Zuba Jari

July 29, 2026
Ma’aikatar Kasuwanci Ta Sin Ta Fitar Da Takarda Game Da Matsayin Sin Kan Abin Da Ake Kira “Samar Da Kayayyaki Fiye Da Kima”

Ma’aikatar Kasuwanci Ta Sin Ta Fitar Da Takarda Game Da Matsayin Sin Kan Abin Da Ake Kira “Samar Da Kayayyaki Fiye Da Kima”

July 29, 2026
Sana’ar Ƙosai: Remi Tinubu Ta Yi Kira ga Burna Boy da Davido Su Taimaka wa Talakawa

Ba Ma Fatan Wani Ɗan Nijeriya Ya Kwana da Yunwa — Remi Tinubu

July 29, 2026
Kotun Ɗaukaka Ƙara Ta Dakatar Da INEC Game Da Soke Rajistar ADC Da Wasu Jam’iyyu

Kotun Ɗaukaka Ƙara Ta Soke Umarnin Cire Rajistar ADC Da Wasu Jam’iyyu Huɗu

July 28, 2026
Kayayyaki Masu Fasahar AI Sun Zamo Sabbin Abubuwa Masu Tasiri A Cinikin Waje Na Kasar Sin

Kayayyaki Masu Fasahar AI Sun Zamo Sabbin Abubuwa Masu Tasiri A Cinikin Waje Na Kasar Sin

July 28, 2026
Ruwa

2027: Gwamnan Kaduna Ya Sanar Da Sabon Mataimakinsa A Zaɓen Gwamna

July 28, 2026
Xi Jinping Ya Yi Bayani Kan Ayyuka Masu Nasaba Da Sinawan Dake Ketare

Xi Jinping Ya Yi Bayani Kan Ayyuka Masu Nasaba Da Sinawan Dake Ketare

July 28, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.