Gwamnan Jihar Nasarawa, Injiniya Abdullahi Sule, ya halarci bikin ƙaddamar da Kamfanin Jinlide•Qiangyu New Energy a birnin Nanchang na lardin Jiangxi, a Kasar Sin, inda ya sake jaddada kudirin gwamnatinsa na ci gaba da jawo manyan masu zuba jari domin bunƙasa masana’antu da ƙara darajar albarkatun ma’adinan jihar Nasarawa.
Gwamnan ya halarci bikin tare da Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, inda ya bayyana ƙaddamar da katafaren kamfanin a matsayin wani muhimmin ci gaba da zai ƙara ƙarfafa haɗin gwiwar tattalin arziki tsakanin kamfanonin ƙasar Sin da jihohin Nijeriya masu albarkatun ma’adinai.
Da yake jawabi a wajen taron, Gwamna Sule ya yabawa shugabannin kamfanin bisa amincewar da suka nuna ga Nijeriya, yana mai cewa gwamnatin jihar za ta ci gaba da samar da yanayi mai kyau ga masu zuba jari ta hanyar aiwatar da manufofi masu gaskiya, inganta ababen more rayuwa da kuma tabbatar da gudanar da harkokin hakar ma’adinai bisa ƙa’ida.
Ya ce manufar gwamnatinsa ita ce ƙarfafa kafa masana’antun da za su riƙa sarrafa albarkatun ma’adinai a cikin Jihar Nasarawa maimakon fitar da su a ɗanye, domin ƙara musu daraja, samar da ayyukan yi ga matasa, inganta musayar fasaha da kuma bunƙasa tattalin arzikin jihar da na ƙasa baki ɗaya.
Jajircewar gwamnatin Sule wajen inganta yanayin zuba jari ta fara haifar da sakamako, inda manyan kamfanonin ƙasar Sin suka fara kafa masana’antun sarrafa lithium a jihar. A shekarar 2024, Kamfanin Avatar New Energy ya ƙaddamar da masana’antar sarrafa lithium mai ƙarfin sarrafa tan 4,000 a kowace rana.
Haka kuma, a ranar 2 ga Yuli, 2026, Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya ƙaddamar da katafaren Kamfanin Diamond New Energy da ke ƙaramar hukumar Nasarawa, wanda aka gina kan jarin dala miliyan 250 na Amurka. Kamfanin na da ƙarfin sarrafa tan 6,000 na lithium a kowace rana, kuma ana kallonsa a matsayin ɗaya daga cikin manyan masana’antun sarrafa lithium a Afirka.
Baya ga waɗannan, akwai wasu kamfanonin hakar lithium da dama da ke gudanar da ayyukansu a Jihar Nasarawa, lamarin da ya ƙara tabbatar da matsayin jihar a matsayin cibiyar masana’antar ma’adinai a Nijeriya.
A yayin ziyarar da ya kai Kamfanin Jinlide•Qiangyu New Energy, Gwamna Sule da tawagarsa sun zagaya sassa daban-daban na kamfanin, inda suka shaida yadda ake amfani da sabbin fasahohi wajen sarrafa kayayyaki tare da bin ƙa’idojin tabbatar da inganci.
Gwamnan ya bayyana gamsuwarsa da irin ci gaban fasahar da ya gani, yana mai cewa gwamnatin jihar za ta ci gaba da ƙarfafa haɗin gwiwa da kamfanonin ƙasar Sin tare da neman rattaba hannu kan ƙarin yarjejeniyoyin fahimtar juna domin faɗaɗa damar zuba jari a fannonin ma’adinai da masana’antu.
A ƙarshen bikin, shugabannin Kamfanin Jinlide•Qiangyu New Energy sun karrama Gwamna Abdullahi Sule da lambar yabo ta musamman saboda gudummawar da yake bayarwa wajen ƙarfafa haɗin gwiwar ƙasa da ƙasa da kuma jawo masu zuba jari zuwa Jihar Nasarawa.
Masu lura da al’amura na ganin cewa ci gaba da zuwan irin waɗannan manyan masana’antun zai taimaka wajen mayar da Jihar Nasarawa cibiyar sarrafa lithium da sauran muhimman ma’adinai a Nijeriya, tare da samar da dubban ayyukan yi da bunƙasa tattalin arziki mai ɗorewa.














