• English
  • Business News
Saturday, November 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Birtaniya Na Son Taimaka Wa Nijeriya Ta Farfado – Atiku 

by Sadiq
3 years ago
Birtaniya

Dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar PDP, Atiku Abubakar, ya ce ya samu kwarin guiwa sosai da irin kwazon da Birtaniya ke da shi na ganin Nijeriya ta farfado ta kowane fanni.

Atiku, ya bayyana hakan ne a shafinsa na Twitter, bayan ziyarar da ya kai Birtaniya domin ganawa da wasu jami’an gwamnatin.

  • Babu Gaskiya A Labarin Cewar G-5 Ta Goyi Bayan Takarar Atiku – Samuel Ortom
  • Buhari Ya Raka Tawagar Yakin Neman Zaben Tinubu Jihar Yobe

A ranar Litinin ne dan takarar na PDP ya tafi Birtaniya bisa gayyatar da gwamnatin kasar ta yi masa.

A yayin ziyarar ta kwanaki biyu, Atiku zai tattauna da jami’an gwamnatin Birtaniya da kuma Archbishop na Canterbury, Justin Welby.

Atiku ya bayyana cewa ya gana da manyan jami’an gwamnatin Birtaniya da kuma Hon. Andrew Mitchell MP – Ministan Ci Gaban Afirka a Ofishin Harkokin Waje.

LABARAI MASU NASABA

Sanata Barau Zai Yi Ƙarar Zargin Karɓar Cin Hancin Dala Miliyan 10

Shugaba Tinubu Da Shugaban Ƙasar Saliyo, Sun Yi Ganawar Sirri A Abuja

Ya kara da cewa ya bayyana musu hangen nesansa game da Nijeriya kamar yadda ya shirye sauya fasalin kasar nan.

“Na gana da Hon. Andrew Mitchell MP – Ministan Ci Gaban Afirka a Ofishin Harkokin Waje, tare da wasu manyan jami’an gwamnatin Birtaniya.

“Abin farin ciki ne na bayyana ra’ayina game da yadda ake son taimakon Nijeriya.

“Na nemi hadin gwiwarsu kuma na samu kwarin gwiwa daga irin kwazon da gwamnatin Birtaniya ke da shi na taimaka wa Nijeriya ta farfado a kowane fanni,” -AA.

Da yake karin haske kan muhimmancin ziyarar, dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar PDP, ya kai Birtaniya, daraktan yada labaran kwamitin yakin neman zaben PDP, Dele Momodu, ya ce Birtaniya na da yakini mai kyau a kan Atiku shi ya sa ta gayyace shi.

Da farko dai an fara yada rade-radin cewar Atiku ya tafi Amurka ne sakamakon rashin lafiya da yake fama da ita.

Sai dai PDP ta musanta wannan zargi inda ta ce ya fice daga kasar nan ne sakamakon goron gayyata da aka aike masa.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Sanata Barau Zai Yi Ƙarar Zargin Karɓar Cin Hancin Dala Miliyan 10
Manyan Labarai

Sanata Barau Zai Yi Ƙarar Zargin Karɓar Cin Hancin Dala Miliyan 10

November 8, 2025
Shugaba Tinubu Da Shugaban Ƙasar Saliyo, Sun Yi Ganawar Sirri A Abuja
Manyan Labarai

Shugaba Tinubu Da Shugaban Ƙasar Saliyo, Sun Yi Ganawar Sirri A Abuja

November 8, 2025
Majalisa Ta Ƙaryata Karɓar Dala Miliyan 10 Don Daƙile Tantance Shugaban NERC
Manyan Labarai

Majalisa Ta Ƙaryata Karɓar Dala Miliyan 10 Don Daƙile Tantance Shugaban NERC

November 8, 2025
Next Post
Tinubu Ne Kadai Zai Iya Magance Rashin Tsaro Da Tabarbarewar Tattalin Arziki – Buhari 

Tinubu Ne Kadai Zai Iya Magance Rashin Tsaro Da Tabarbarewar Tattalin Arziki – Buhari 

LABARAI MASU NASABA

Sanata Barau Zai Yi Ƙarar Zargin Karɓar Cin Hancin Dala Miliyan 10

Sanata Barau Zai Yi Ƙarar Zargin Karɓar Cin Hancin Dala Miliyan 10

November 8, 2025
Maganin Nankarwa (4)

Maganin Nankarwa (4)

November 8, 2025
Kotu Ta Yanke Wa Wata Budurwa Hukuncin Shekaru 4 A Kano, Duba Laifinta

Kotu Ta Yanke Wa Wata Budurwa Hukuncin Shekaru 4 A Kano, Duba Laifinta

November 8, 2025
NELFUND Ta Ce Dalibai Miliyan Daya Ne Suka Nemi Tallafin Kudin Karatu

NELFUND Ta Ce Dalibai Miliyan Daya Ne Suka Nemi Tallafin Kudin Karatu

November 8, 2025
Shugaba Tinubu Da Shugaban Ƙasar Saliyo, Sun Yi Ganawar Sirri A Abuja

Shugaba Tinubu Da Shugaban Ƙasar Saliyo, Sun Yi Ganawar Sirri A Abuja

November 8, 2025
Majalisa Na Binciken Kwangilar Titin Naira Biliyan 1.46 Da Aka Yi Watsi Da Shi A Kaduna

Matsalar Tsaro: Yadda Dabarun Uba Sani Suka Mayar Da Tsoro Zuwa Kyakkyawar Fata A Jihar Kaduna

November 8, 2025
Majalisa Ta Ƙaryata Karɓar Dala Miliyan 10 Don Daƙile Tantance Shugaban NERC

Majalisa Ta Ƙaryata Karɓar Dala Miliyan 10 Don Daƙile Tantance Shugaban NERC

November 8, 2025
An Fara Binciken Batan Dan Bautar Kasa A Bayelsa

An Fara Binciken Batan Dan Bautar Kasa A Bayelsa

November 8, 2025
An Damke Mutum 11 Da Ake Zargi Da Kisan Wani Matashi A Bauchi

An Damke Mutum 11 Da Ake Zargi Da Kisan Wani Matashi A Bauchi

November 8, 2025
Shugaban Kasa Yana Bibiyar Zanga-zangar Matsin Rayuwa – Minista

Shirin Shugaba Tinubu Na ‘Renewed Hope’ Zai Karfafa Wa Manoma Gwiwa – Oyebanji

November 7, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.