ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Bunkasar Tattalin Arzikin Sin: Ya Kamata Afirka Ta Dama Idan Dama Ta Samu

by Sulaiman
5 months ago
Afirka

Bunkasar tattalin arzikin kasar Sin da kashi 5 cikin dari a shekarar 2025 cikin yanayi mai sarkakiya na kasa da kasa, wanda ya kunshi sauye‑sauyen kasuwanci, hauhawar farashi a duniya, kalubalen basussuka, da rikice‑rikicen tattalin arziki tsakanin manyan kasashe, wata dama ce ga kasashen Afirka da ta kamata su dama a ciki ba tare da sanya ba.

Sakamakon yanayi mai rikitarwa da duniya ke kara-kaina a ciki, ci gaban tattalin arzikin Sin ya zama wani ginshiki na samar da kwanciyar hankali a bangaren kasuwancin duniya musamman ma yadda ya ci gaba da ba da gudunmawar kashi 30 cikin dari na jimillar tattalin arzikin duniya baki daya. Afirka, wadda ke da alaka mai zurfi da kasar Sin ta fuskar kasuwanci da zuba jari, na iya kara cin gajiyar hakan ta hanyar albarkatun kasa, musamman ma’adanai, makamashi, da kayayyakin noma, ko da kuwa kasuwannin wasu abokan huldarsu sun yi tutsu.

Matukar an samar da tsayayyun manufofi da yanayi mai dacewa da zuba jari, wannan zai kara bai wa Afirka damar jawo zuba jari kai-tsaye daga kasar Sin, musamman a fannonin da aka rika aka kulla kawance kamar ababen more rayuwa, masana’antu, makamashi, fasahar zamani da sauransu.

ADVERTISEMENT

Kazalika, sauye‑sauyen da kasar Sin take ta yekuwar tabbatarwa a tsarin tafiyar da tattalin arzikin duniya domin karfafa kasashe masu tasowa da kokarin rage dogaro da wuri guda wajen samar da kayayyaki, na kara bude wa Afirka kofa wajen shiga tsarin samar da kayayyaki na duniya, ta yadda nahiyar za ta samu damar fitar da kayayyakin da ta sarrafa maimakon dogaro da cinikin danyen albarkatun kasa kawai.

Sai dai kuma, domin kar wannan dama ta zama “ga koshi ga kwanan yunwa”, wajibi ne gwamnatocin Afirka su kara yin hobbasa a bangaren tsara muradun tattalin arziki na dogon zango, da dabarun fuskantar kalubalen da za su biyo baya musamman daga sauran kasuwannin duniya da kuma sauyin yanayi. Mun riga mun ga makirce-makircen da ake ta kulla wa manyan kasashen nahiyar bisa farkawarsu da kuma alakar da suke zurfafawa da Sin a matsayin aminiyarsu. Ana ta kokarin mayar da hannun agogo baya ta hanyar rura wutar rikicin addini da kabilanci, har ma da na bangaranci.

LABARAI MASU NASABA

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

A takaice dai, a cikin wannan yanayi mai sarkakiya na kasa da kasa, ci gaban da tattalin arzikin kasar Sin ya samu na kashi 5 cikin dari a 2025 wani ginshiki ne da Afirka za ta iya dogaro da shi, saboda Sin ita ce babbar abokiyar cinikin nahiyar har na tsawon kimanin shekaru 16 a jere, sannan ga manufar soke haraji ga kayayyakin galibin kasashen nahiyar masu huldar diflomasiyya da ita da ake kawowa kasuwarta. Amma kuma nasarar hakan za ta rataya ce kan iya daidaita damammakin da kuma kalubale cikin tsari, hangen nesa, da ingantaccen tsarin shugabanci na-gari. (Abdulrazaq Yahuza Jere)

Afirka
Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    An Fara Gasar Tseren Dawakai Ta ‘Renewed Hope’ da Sabon Salo A Kano
  • Sulaiman
    Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace
  • Sulaiman
    ’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin
  • Sulaiman
    Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

MASU ALAKA

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace
Daga Birnin Sin

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin
Daga Birnin Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi
Daga Birnin Sin

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Next Post
Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed

Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed

LABARAI MASU NASABA

Sojoji Sun Kama Mai Kai Wa Ƴan Ta’adda Kayan Aiki A Zamfara

Sojoji Sun Kama Mai Kai Wa Ƴan Ta’adda Kayan Aiki A Zamfara

June 25, 2026
Kotu Ta Ɗege Shari’ar Ganduje Da Wasu Mutum 7 Zuwa 14 Ga Oktoba 2026

Kotu Ta Ɗege Shari’ar Ganduje Da Wasu Mutum 7 Zuwa 14 Ga Oktoba 2026

June 25, 2026
An Fara Gasar Tseren Dawakai Ta ‘Renewed Hope’ da Sabon Salo A Kano

An Fara Gasar Tseren Dawakai Ta ‘Renewed Hope’ da Sabon Salo A Kano

June 25, 2026
APC Ta Dage Yakin Zaben Shugaban Kasarta A Kano

An Dakatar Da Shugaban APC Na Kebbi Da Kwamishina Kan Zaɓen Cike Gurbin Zuru

June 25, 2026
Ndume Ya Bayyana Dalilin Da Ya Sa Yake Goyon Bayan Ƙudirin Kafa ‘Yansandan Jihohi

Ndume Ya Bayyana Dalilin Da Ya Sa Yake Goyon Bayan Ƙudirin Kafa ‘Yansandan Jihohi

June 25, 2026
EFCC Za Ta Gurfanar Da Shugaban Miyetti Allah Kan Zargin Almundahanar Dala Miliyan 2.53

EFCC Za Ta Gurfanar Da Shugaban Miyetti Allah Kan Zargin Almundahanar Dala Miliyan 2.53

June 25, 2026
Maroko Ta Zama Ƙasa Ta Farko Daga Afirka Da Ta Tsallaka Zuwa Zagaye Na 32 A Gasar Kofin Duniya

Maroko Ta Zama Ƙasa Ta Farko Daga Afirka Da Ta Tsallaka Zuwa Zagaye Na 32 A Gasar Kofin Duniya

June 25, 2026
Zan Ware 10bn Don Inganta Ilimin Matasa Idan Na Ci Zabe – Atiku

‘Yan Nijeriya Ba Sa Bukatar ‘Yan Jarida Su Faɗa Musu Suna Jin Yunwa — Atiku

June 25, 2026
Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.