Kungiyoyin kwadago na NLC da TUC, sun janye yajin aikin da suka fara a fadin kasar nan.
Wata majiya mai tushe daga NLC ya shaida wa LEADERSHIP cewa kungiyar kwadago ta dage yajin aikin ne na ‘yan kwanaki.
Ayyukan masana’antu da harkokin tattalin arziki da gwamnati sun durkushe a fadin kasar nan bayan fara yajin aikin da kwana biyu.
Kungiyar kwadago ta dakatar da yajin aikin ne, bayan taron majalisar zartarwa na kasa (NEC), da suka yi a Abuja a ranar Talata.
Kungiyar ta cimma yarjejeniya da gwamnatin tarayya kan sabon mafi karancin albashi a ranar Litinin.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp