ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Sunday, December 21, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Da Gaske Atiku Ya Hakura Da Wike?

by Yusuf Shuaibu
3 years ago
Atiku da Wike

Atiku da Wike

A daidai lokacin da rikicin jam’iyyar PDP ke ci gaba da ta’azzara, dan takarar shugaban kasa a karkashin tutar jam’iyyar PDP, Atiku Abubakar ya ci gaba da shirye-shiryen zaben 2023 bayan ya kasa samun fahimtar juna da Gwamnan Jihar Ribas, Nyesom Wike.

Wannan na zuwa ne bayan samun rahotonin ganawar Gwamnan Ribas da takwarorinsa na jihohin Oyo da Benuwe da Abiya a Landan tare da dan takarar shugaban kasa, wadanda suka dage ba za su goyi bayan Atiku ba a karkashin jam’iyyar matukar aka kasa biya musu bukatocinsu.

  • Kashi 31 Na ‘Yan Nijeriya Ba Su Iya Karatu Da Rubutu Ba ― Gwamnatin Tarayya
  • Da Dumi-Dumi: Jami’an Tsaro Sun Kai Samame Gidan Tukur Mamu

Haka kuma rahotonnin sun bayyana cewa an samu ganawa tsakanin Wike da dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar APC, Bola Tinubu da ‘yan takaran gwamna na APC na jihohin Benuwe da Ribas da kuma Oyo.

ADVERTISEMENT

Ana tsammanin majalisar zantarwa ta PDP za ta gudanar da taro a wannan mako domin tabbatar da yadda za a fara gudanar da yakin neman zaben shugaban kasa kafin ranar 28 ga watan Satumba.

An dai bayyana cewa jam’iyyar ta watsar da mafi yawancin shiryeshiryanta saboda zaman sulhu tsakanin Wike da Atiku.

LABARAI MASU NASABA

2027: Sauya Sheka Zuwa APC Ba Zai Taimaki Tinuba Yin Tazarce Ba – Jam’iyyar ADC

‘Yan Adawa Sun Yi Gargadi Kan Barazanar Dakile Dimokuradiyya Mai Jam’iyyu Da Dama

Wata majiya ta bayyana wa LEADERSHIP dalilan da ya sa shugaban jam’iyyar, Dakta Iyorchia Ayu ya bata wa Wike da wasu rai shi ne, Atiku zai hakura da Wike.

Ayu ya dage a kan ba zai taba sauka daga shugabancin jam’iyyar ba har sai ya cika wa’adin mulkinsa na shekaru hudu, wanda bangaren Wike suka bukaci ya sauka daga mukaminsa, inda ya kada baki ya ce lokacin da suka shiga jam’iyyar PDP a shekarar 1998, gwamnan Jihar Ribas yana yaro. Wike ya mayar wa Ayu martani wanda ya yi gargadin cewa zai taimaka wajen faduwar PDP a zaben 2023.

Majiyar ta kara da cewa Wike ne ya farfado da jam’iyyar PDP lokacin da jiga-jigan jam’iyyar suka kaurace mata a shekarar 2015, inda har ta dawo cikin hayyacinta.

A wannan makon ne, Atiku ya ganawar sirri da ‘yan takarar gwamna a karkashin jam’iyyar a dukkan jihohin kasar nan.

Atiku ya yi wannan ganawa ce tare da mataimakinsa, Gwamnan Jihar Delta, Ifeanyi Okowa a gidansa da ke Asokoro cikin garin Abuja.

A cikin wadada suka halarci ganawar sun hada da ‘yan takaran gwamna a jihohin Kaduna, Filato, Katsina, Legas, Neja, Kano, Sakkwato, Delta, Yobe, Jigawa, Nasarawa, Kwara, Benuwe, Borno, Ebonyi da kuma Zamfara.

Ganawar Atiku da ‘yan takarar ta zo ne bayan da shugabannin jam’iyyar suka bayyana tsarin gudanar da yakin neman zabe. A ganawarsa da ‘yan jarida a Abuja, sakataren jam’iyyar PDP, Hon Debo Ologunagba ya bayyana cewa jam’iyyar ba za ta taba rugujewa ba saboda wani mutum. “Wannan jam’iyyar tana martaba duk wani dan PDP.

Wike ya kasance babban barazana ga Nijeriya ba wai ga jam’iyyar PDP ba. PDP ba ta mutum daya ba ce.

“Dukkan bangarorin jam’iyyar suna aiki tare domin cimma muraduta. Dole mu amince da bukatun kowa saboda kar mu yi asarar sa. Muna tafiya da dukkan ra’ayoyin ‘ya’yan jam’iyyar.

“A hankali mun kusa cimma matsaya. Muna da bambancin ra’ayi, amma ba ma cikin rikici. Muna da rashin amincewa wajen zabi. Babu wata rikici a PDP, amma muna da bambancin ra’ayoyi wanda Dan’adam yake da shi a halittarsa.

“Dole sai mun hada kai za mu iya ceto jam’iyyar. Shugabannin da masu ruwa da tsaki na jam’iyyar sun hada kansu wuri daya kan wannan lamari. Jam’iyyar za ta ci gaba da gudanar da shirye-shiryenta domin ceto kasar nan,” in ji shi.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

2027: Sauya Sheka Zuwa APC Ba Zai Taimaki Tinuba Yin Tazarce Ba – Jam’iyyar ADC
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Sauya Sheka Zuwa APC Ba Zai Taimaki Tinuba Yin Tazarce Ba – Jam’iyyar ADC

December 19, 2025
‘Yan Adawa Sun Yi Gargadi Kan Barazanar Dakile Dimokuradiyya Mai Jam’iyyu Da Dama
Tambarin Dimokuradiyya

‘Yan Adawa Sun Yi Gargadi Kan Barazanar Dakile Dimokuradiyya Mai Jam’iyyu Da Dama

December 19, 2025
Kwankwaso Ya Gana Da Shugabannin NNPP A Kuros Ribas Don Tunkarar Zaɓen 2027
Tambarin Dimokuradiyya

NNPP Ta Buƙaci INEC Ta Yi Watsi Da Tarukan Jam’iyyar Da Kwankwaso Zai Jagoranta

November 28, 2025
Next Post
“Akwai Matsala Game Da Bakin Da Ke Kwararowa Jihar Kano”

“Akwai Matsala Game Da Bakin Da Ke Kwararowa Jihar Kano”

LABARAI MASU NASABA

Tinubu

Dambarwar Naɗa Muƙamai Da Soke Su A Gwamnatin Tinubu

December 21, 2025
Zaben Fidda Gwani A APC: Sanatocin Jigawa Sun Rasa Tikitin Komawa Majalisa

APC Za Ta Gudanar Da Babban Taronta Na Kasa A Watan Maris

December 21, 2025
Mun Shirya Tsaf Domin Lashe Gasar AFCON Ta Bana – Bassey

Mun Shirya Tsaf Domin Lashe Gasar AFCON Ta Bana – Bassey

December 21, 2025
Sarakuna Na Da Rawar Takawa Wajen Kare Muhalli A Nijeriya – Ministan Muhalli

Sarakuna Na Da Rawar Takawa Wajen Kare Muhalli A Nijeriya – Ministan Muhalli

December 21, 2025
Me Ya Sa Ake Fifita Ilimin Boko A Kan Na Addini?

Me Ya Sa Ake Fifita Ilimin Boko A Kan Na Addini?

December 21, 2025
Yadda Itacen Dorawa Ke Warkar Da Cututtuka Daban-daban

Yadda Itacen Dorawa Ke Warkar Da Cututtuka Daban-daban

December 21, 2025
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

An Cafke Wani Mutum Da Ya Lakada Wa Dansa Duka Har Lahira A Edo

December 21, 2025
Bambance-bambancenmu Shine Ƙarfinmu — Uba Sani

Bambance-bambancenmu Shine Ƙarfinmu — Uba Sani

December 21, 2025
Kotu Ta Fara Sauraren Korafe-korafen Dalibai A Kan Jami’ar MAAUN

Kotu Ta Fara Sauraren Korafe-korafen Dalibai A Kan Jami’ar MAAUN

December 21, 2025
Tinubu Ya Sauya Sunan Jami’ar Azare Don Karrama Sheikh Dahiru Usman Bauchi

Tinubu Ya Sauya Sunan Jami’ar Azare Don Karrama Sheikh Dahiru Usman Bauchi

December 20, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.