• English
  • Business News
Sunday, September 14, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Da Gaske Atiku Ya Hakura Da Wike?

by Yusuf Shuaibu
3 years ago
in Tambarin Dimokuradiyya
0
Da Gaske Atiku Ya Hakura Da Wike?

Atiku da Wike

Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A daidai lokacin da rikicin jam’iyyar PDP ke ci gaba da ta’azzara, dan takarar shugaban kasa a karkashin tutar jam’iyyar PDP, Atiku Abubakar ya ci gaba da shirye-shiryen zaben 2023 bayan ya kasa samun fahimtar juna da Gwamnan Jihar Ribas, Nyesom Wike.

Wannan na zuwa ne bayan samun rahotonin ganawar Gwamnan Ribas da takwarorinsa na jihohin Oyo da Benuwe da Abiya a Landan tare da dan takarar shugaban kasa, wadanda suka dage ba za su goyi bayan Atiku ba a karkashin jam’iyyar matukar aka kasa biya musu bukatocinsu.

  • Kashi 31 Na ‘Yan Nijeriya Ba Su Iya Karatu Da Rubutu Ba ― Gwamnatin Tarayya
  • Da Dumi-Dumi: Jami’an Tsaro Sun Kai Samame Gidan Tukur Mamu

Haka kuma rahotonnin sun bayyana cewa an samu ganawa tsakanin Wike da dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar APC, Bola Tinubu da ‘yan takaran gwamna na APC na jihohin Benuwe da Ribas da kuma Oyo.

Ana tsammanin majalisar zantarwa ta PDP za ta gudanar da taro a wannan mako domin tabbatar da yadda za a fara gudanar da yakin neman zaben shugaban kasa kafin ranar 28 ga watan Satumba.

An dai bayyana cewa jam’iyyar ta watsar da mafi yawancin shiryeshiryanta saboda zaman sulhu tsakanin Wike da Atiku.

Labarai Masu Nasaba

Rudani Ya Kunno Kai Yayin Da INEC Ta Ki Amincewa Da Shugabancin ADC

‘Yan Nijeriya Suna Shan Wahala A Lokacin Da Gwamnatin Tinubu Ta Fi Damuwa Da Aljihunta – Sule Lamido

Wata majiya ta bayyana wa LEADERSHIP dalilan da ya sa shugaban jam’iyyar, Dakta Iyorchia Ayu ya bata wa Wike da wasu rai shi ne, Atiku zai hakura da Wike.

Ayu ya dage a kan ba zai taba sauka daga shugabancin jam’iyyar ba har sai ya cika wa’adin mulkinsa na shekaru hudu, wanda bangaren Wike suka bukaci ya sauka daga mukaminsa, inda ya kada baki ya ce lokacin da suka shiga jam’iyyar PDP a shekarar 1998, gwamnan Jihar Ribas yana yaro. Wike ya mayar wa Ayu martani wanda ya yi gargadin cewa zai taimaka wajen faduwar PDP a zaben 2023.

Majiyar ta kara da cewa Wike ne ya farfado da jam’iyyar PDP lokacin da jiga-jigan jam’iyyar suka kaurace mata a shekarar 2015, inda har ta dawo cikin hayyacinta.

A wannan makon ne, Atiku ya ganawar sirri da ‘yan takarar gwamna a karkashin jam’iyyar a dukkan jihohin kasar nan.

Atiku ya yi wannan ganawa ce tare da mataimakinsa, Gwamnan Jihar Delta, Ifeanyi Okowa a gidansa da ke Asokoro cikin garin Abuja.

A cikin wadada suka halarci ganawar sun hada da ‘yan takaran gwamna a jihohin Kaduna, Filato, Katsina, Legas, Neja, Kano, Sakkwato, Delta, Yobe, Jigawa, Nasarawa, Kwara, Benuwe, Borno, Ebonyi da kuma Zamfara.

Ganawar Atiku da ‘yan takarar ta zo ne bayan da shugabannin jam’iyyar suka bayyana tsarin gudanar da yakin neman zabe. A ganawarsa da ‘yan jarida a Abuja, sakataren jam’iyyar PDP, Hon Debo Ologunagba ya bayyana cewa jam’iyyar ba za ta taba rugujewa ba saboda wani mutum. “Wannan jam’iyyar tana martaba duk wani dan PDP.

Wike ya kasance babban barazana ga Nijeriya ba wai ga jam’iyyar PDP ba. PDP ba ta mutum daya ba ce.

“Dukkan bangarorin jam’iyyar suna aiki tare domin cimma muraduta. Dole mu amince da bukatun kowa saboda kar mu yi asarar sa. Muna tafiya da dukkan ra’ayoyin ‘ya’yan jam’iyyar.

“A hankali mun kusa cimma matsaya. Muna da bambancin ra’ayi, amma ba ma cikin rikici. Muna da rashin amincewa wajen zabi. Babu wata rikici a PDP, amma muna da bambancin ra’ayoyi wanda Dan’adam yake da shi a halittarsa.

“Dole sai mun hada kai za mu iya ceto jam’iyyar. Shugabannin da masu ruwa da tsaki na jam’iyyar sun hada kansu wuri daya kan wannan lamari. Jam’iyyar za ta ci gaba da gudanar da shirye-shiryenta domin ceto kasar nan,” in ji shi.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: AtikuPDPRikiciSiyasaSulhuWike
ShareTweetSendShare
Previous Post

Rayuwata A Shekara 70 -Mai Martaba Etsu Nupe

Next Post

“Akwai Matsala Game Da Bakin Da Ke Kwararowa Jihar Kano”

Related

Fursunoni Ba Za Su Samu Damar Kada Kuri’a Ba A Zaben 2023 – INEC
Tambarin Dimokuradiyya

Rudani Ya Kunno Kai Yayin Da INEC Ta Ki Amincewa Da Shugabancin ADC

1 week ago
‘Yan Nijeriya Suna Shan Wahala A Lokacin Da Gwamnatin Tinubu Ta Fi Damuwa Da Aljihunta – Sule Lamido
Tambarin Dimokuradiyya

‘Yan Nijeriya Suna Shan Wahala A Lokacin Da Gwamnatin Tinubu Ta Fi Damuwa Da Aljihunta – Sule Lamido

1 week ago
Daraktoci Da Jami’an FCT 7 Na Fuskantar Tuhume-tuhume Kan Badakar Fili
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Idan Kana Son Tarwatsa PDP, To Ka Dawo Da Peter Obi – Wike

1 week ago
ADC Ta Bukaci Tinubu Ya Kafa Dokar Ta Baci A Katsina Da Zamfara Kan Rashin Tsaro
Tambarin Dimokuradiyya

ADC Ta Bukaci Tinubu Ya Kafa Dokar Ta Baci A Katsina Da Zamfara Kan Rashin Tsaro

2 weeks ago
katin zabe
Tambarin Dimokuradiyya

INEC Ta Bayyana Damuwarta Kan Katunan Zabe 360,000 Da Ba A Karba Ba A Kano

2 weeks ago
Jam’iyyar PDP Ta Janye Daga Shiga Zaɓen Ƙananan Hukumomi A Kebbi
Tambarin Dimokuradiyya

Shugabannin PDP Sun Shiga Dimuwa Yayin Da APC Ke Zawarcin Wasu Gwamnoninsu

2 weeks ago
Next Post
“Akwai Matsala Game Da Bakin Da Ke Kwararowa Jihar Kano”

“Akwai Matsala Game Da Bakin Da Ke Kwararowa Jihar Kano”

LABARAI MASU NASABA

Jagororin Kamfanonin Ketare Sun Nuna Gamsuwa Dangane Da Zuba Jari A Kasar Sin

Jagororin Kamfanonin Ketare Sun Nuna Gamsuwa Dangane Da Zuba Jari A Kasar Sin

September 14, 2025
Bayan Fara Kamen Mabarata, An Samu Dalar Amurka, Wuƙa A Kwara

Bayan Fara Kamen Mabarata, An Samu Dalar Amurka, Wuƙa A Kwara

September 14, 2025
Ina Fatan Watsi Da Harkar Fim Nan Gaba —Umar Hassan

Ina Fatan Watsi Da Harkar Fim Nan Gaba —Umar Hassan

September 14, 2025
An Kammala Baje Kolin Hada-Hadar Cinikayyar Hidimomi Na Sin Na Shekarar 2025

An Kammala Baje Kolin Hada-Hadar Cinikayyar Hidimomi Na Sin Na Shekarar 2025

September 14, 2025
Fadar Shugaban Ƙasa Ta Sanar Da Dalilin Korar Hadimin Shettima Kan Bunƙasa Tattalin Arziƙi

Fadar Shugaban Ƙasa Ta Sanar Da Dalilin Korar Hadimin Shettima Kan Bunƙasa Tattalin Arziƙi

September 14, 2025
Shugabanci A Nijeriya: A Ina Ne Gizo Ke Saƙar?

Shugabanci A Nijeriya: A Ina Ne Gizo Ke Saƙar?

September 14, 2025
Me Ya Sa Shawarar Tsarin Shugabancin Duniya Ta Samu Goyon Baya Daga Sassan Kasa Da Kasa

Me Ya Sa Shawarar Tsarin Shugabancin Duniya Ta Samu Goyon Baya Daga Sassan Kasa Da Kasa

September 14, 2025
Sama Da Fam Biliyan Uku Aka Kashe A Firimiyar Ingila Wajen Sayen Ƴan Wasa

Sama Da Fam Biliyan Uku Aka Kashe A Firimiyar Ingila Wajen Sayen Ƴan Wasa

September 14, 2025
Me Ya Sa Bayern Liverkusen Ta Kori Erik Ten Hag Bayan Wasanni Biyu?

Me Ya Sa Bayern Liverkusen Ta Kori Erik Ten Hag Bayan Wasanni Biyu?

September 14, 2025
An Karrama Fitattun Fina-Finai A Bikin “Golden Panda” Da Ya Gudana A Lardin Sichuan Na Kasar Sin

An Karrama Fitattun Fina-Finai A Bikin “Golden Panda” Da Ya Gudana A Lardin Sichuan Na Kasar Sin

September 14, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.